< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
Ingoma yemiqanso. Labo abamethembayo uThixo banjengentaba iZiyoni, yona enganyikinyekiyo, emi kuze kube laphakade.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Njengezintaba ezigombolozele iJerusalema, ngokunjalo uThixo uzungeza abantu bakhe manje kuze kube laphakade.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Intonga yobukhosi eyababi kayiyikusala ezweni elabelwe abalungileyo, ngoba abalungileyo bangaqabuka sebesebenzisa izandla zabo ukwenza okubi.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Yenza okuhle, awu Thixo, kulabo abalungileyo, kulabo abaqotho enhliziyweni
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
kodwa labo abaphambukela ezindleleni ezitshekileyo uThixo uzabaxotsha kanye labenzi bobubi. Ukuthula kakube ku-Israyeli.

< Zabura 125 >