< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
Cantique de Mahaloth. Ceux qui se confient en l'Eternel sont comme la montagne de Sion, qui ne peut être ébranlée, et qui se soutient à toujours.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Quant à Jérusalem, il y a des montagnes à l'entour d'elle, et l'Eternel est à l'entour de son peuple, dès maintenant et à toujours.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Car la verge de la méchanceté ne reposera point sur le lot des justes; de peur que les justes ne mettent leurs mains à l'iniquité.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Eternel, bénis les gens de bien et ceux dont le cœur est droit.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Mais quant à ceux qui tordent leurs sentiers obliques, l'Eternel les fera marcher avec les ouvriers d'iniquité. La paix [sera] sur Israël.

< Zabura 125 >