< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
Cantique des montées. Ceux qui se confient en Yahweh sont comme la montagne de Sion: elle ne chancelle point, elle est établie pour toujours.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Jérusalem a autour d’elle une ceinture de montagnes: ainsi Yahweh entoure son peuple, dès maintenant et à jamais.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Le sceptre des méchants ne restera pas sur l’héritage des justes, afin que les justes ne portent pas aussi leurs mains vers l’iniquité.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Yahweh, répands tes bontés sur les bons, et sur ceux qui ont le cœur droit.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Mais sur ceux qui se détournent en des voies tortueuses, que Yahweh les abandonne avec ceux qui font le mal! Paix sur Israël!

< Zabura 125 >