< Zabura 125 >
1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
A song of ascents. Those who trust in Yahweh are like Mount Zion, unshakable, forever enduring.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
As the mountains surround Jerusalem, so Yahweh surrounds his people now and forever.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
The scepter of wickedness must not rule in the land of the righteous. Otherwise the righteous might do what is wrong.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Do good, Yahweh, to those who are good and to those who are upright in their hearts.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
But as for those who turn aside to their crooked ways, Yahweh will lead them away with the evildoers. May peace be on Israel.