< Zabura 124 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba, bari Isra’ila yă ce,
canticum graduum huic David nisi quia Dominus erat in nobis dicat nunc Israhel
2 da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba sa’ad da aka auka mana,
nisi quia Dominus erat in nobis cum exsurgerent in nos homines
3 sa’ad da fushinsu ya ƙuna a kanmu, ai, da sun haɗiye mu da rai;
forte vivos degluttissent nos cum irasceretur furor eorum in nos
4 da rigyawa ta kwashe mu, da ambaliya ta rufe mu.
forsitan aqua absorbuisset nos
5 Da ruwa mai hauka ya share mu ƙaf.
torrentem pertransivit anima nostra forsitan pertransisset anima nostra aquam intolerabilem
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.
benedictus Dominus qui non dedit nos in captionem dentibus eorum
7 Mun tsira kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta; an tsinke tarko, muka kuwa tsira.
anima nostra sicut passer erepta est de laqueo venantium laqueus contritus est et nos liberati sumus
8 Taimakonmu yana a sunan Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
adiutorium nostrum in nomine Domini qui fecit caelum et terram

< Zabura 124 >