< Zabura 124 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba, bari Isra’ila yă ce,
Se il Signore non fosse stato con noi, - lo dica Israele - Canto delle ascensioni. Di Davide.
2 da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba sa’ad da aka auka mana,
se il Signore non fosse stato con noi, quando uomini ci assalirono,
3 sa’ad da fushinsu ya ƙuna a kanmu, ai, da sun haɗiye mu da rai;
ci avrebbero inghiottiti vivi, nel furore della loro ira.
4 da rigyawa ta kwashe mu, da ambaliya ta rufe mu.
Le acque ci avrebbero travolti; un torrente ci avrebbe sommersi,
5 Da ruwa mai hauka ya share mu ƙaf.
ci avrebbero travolti acque impetuose.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.
Sia benedetto il Signore, che non ci ha lasciati, in preda ai loro denti.
7 Mun tsira kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta; an tsinke tarko, muka kuwa tsira.
Noi siamo stati liberati come un uccello dal laccio dei cacciatori: il laccio si è spezzato e noi siamo scampati.
8 Taimakonmu yana a sunan Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
Il nostro aiuto è nel nome del Signore che ha fatto cielo e terra.