< Zabura 124 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba, bari Isra’ila yă ce,
Nyanyian ziarah Daud. Bagaimana seandainya TUHAN tidak memihak kita? Hai Israel, jawablah demikian:
2 da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba sa’ad da aka auka mana,
"Seandainya TUHAN tidak memihak kita waktu kita diserang lawan,
3 sa’ad da fushinsu ya ƙuna a kanmu, ai, da sun haɗiye mu da rai;
maka kita sudah ditelan hidup-hidup, oleh kemarahan mereka yang meluap-luap.
4 da rigyawa ta kwashe mu, da ambaliya ta rufe mu.
Maka kita sudah dihanyutkan banjir, dan digenangi air;
5 Da ruwa mai hauka ya share mu ƙaf.
maka kita sudah mati tenggelam dalam pusaran air yang seram."
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.
Mari kita bersyukur kepada TUHAN, sebab Ia tidak membiarkan kita dimusnahkan lawan.
7 Mun tsira kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta; an tsinke tarko, muka kuwa tsira.
Kita seperti burung yang lepas dari jerat pemburu, jerat itu sudah putus, dan kita pun lepas!
8 Taimakonmu yana a sunan Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
Pertolongan kita datang dari TUHAN yang menciptakan langit dan bumi.

< Zabura 124 >