< Zabura 123 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna gare ka, gare ka da kursiyinka yake cikin sama.
J’ai levé mes yeux vers vous, qui habitez dans les cieux.
2 Kamar yadda idanun bayi suna duban hannun maigidansu, kamar yadda idanun baiwa suna duban hannun uwargijiyarta, haka idanunmu suna duban Ubangiji Allahnmu, sai ya nuna mana jinƙansa.
Voyez, comme les yeux des esclaves sont fixés sur les mains de leurs maîtres.
3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, gama mun jimre da reni mai yawa.
Ayez pitié de nous, Seigneur, ayez pitié de nous; parce que nous avons été entièrement remplis de dédain:
4 Mun jimre da wulaƙanci daga masu girman kai, reni mai yawa daga masu fariya.
Parce que notre âme en a été entièrement remplie: nous sommes un opprobre pour ceux qui sont dans l’abondance, et un dédain pour les superbes.