< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Canción de las gradas. Alzaré mis ojos a los montes, de donde vendrá mi socorro.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Mi socorro viene de parte del SEÑOR, que hizo los cielos y la tierra.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
No dará tu pie al resbaladero; ni se dormirá el que te guarda.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
He aquí, no se adormecerá ni dormirá el que guarda a Israel.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
El SEÑOR será tu guardador; el SEÑOR será tu sombra a tu mano derecha.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
El sol no te fatigará de día, ni la luna de noche.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
El SEÑOR te guardará de todo mal; el guardará tu alma.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
El SEÑOR guardará tu salida y tu entrada, desde ahora y para siempre.

< Zabura 121 >