< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Возведох очи мои в горы, отнюдуже приидет помощь моя.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Помощь моя от Господа, сотворшаго небо и землю.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Не даждь во смятение ноги твоея, ниже воздремлет храняй тя:
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
се, не воздремлет, ниже уснет храняй Израиля.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Господь сохранит тя, Господь покров твой на руку десную твою.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Во дни солнце не ожжет тебе, ниже луна нощию.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Господь сохранит тя от всякаго зла, сохранит душу твою Господь:
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Господь сохранит вхождение твое и исхождение твое, отныне и до века.

< Zabura 121 >