< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Песнь восхождения. Возвожу очи мои к горам, откуда придет помощь моя.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Помощь моя от Господа, сотворившего небо и землю.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Не даст Он поколебаться ноге твоей, не воздремлет хранящий тебя;
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
не дремлет и не спит хранящий Израиля.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Господь - хранитель твой; Господь - сень твоя с правой руки твоей.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Днем солнце не поразит тебя, ни луна ночью.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Господь сохранит тебя от всякого зла; сохранит душу твою Господь.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Господь будет охранять выхождение твое и вхождение твое отныне и вовек.

< Zabura 121 >