< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
canticum graduum levavi oculos meos in montes unde veniet auxilium mihi
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
auxilium meum a Domino qui fecit caelum et terram
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
non det in commotionem pedem tuum neque dormitet qui custodit te
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
ecce non dormitabit neque dormiet qui custodit Israhel
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Dominus custodit te Dominus protectio tua super manum dexteram tuam
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
per diem sol non uret te neque luna per noctem
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Dominus custodit te ab omni malo custodiat animam tuam Dominus
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Dominus custodiat introitum tuum et exitum tuum ex hoc nunc et usque in saeculum