< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Canticum graduum. Levavi oculos meos in montes, unde veniet auxilium mihi.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Auxilium meum a Domino, qui fecit cælum et terram.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Non det in commotionem pedem tuum: neque dormitet qui custodit te.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Ecce non dormitabit neque dormiet, qui custodit Israel.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Dominus custodit te, Dominus protectio tua, super manum dexteram tuam.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Per diem sol non uret te: neque luna per noctem.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Dominus custodit te ab omni malo: custodiat animam tuam Dominus.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Dominus custodiat introitum tuum, et exitum tuum: ex hoc nunc, et usque in sæculum.

< Zabura 121 >