< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Canto dei pellegrinaggi. Io alzo gli occhi ai monti… Donde mi verrà l’aiuto?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Il mio aiuto vien dall’Eterno che ha fatto il cielo e la terra.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Egli non permetterà che il tuo piè vacilli; colui che ti protegge non sonnecchierà.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Ecco, colui che protegge Israele non sonnecchierà né dormirà.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
L’Eterno è colui che ti protegge; l’Eterno è la tua ombra; egli sta alla tua destra.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Di giorno il sole non ti colpirà, né la luna di notte.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
L’Eterno ti proteggerà da ogni male, egli proteggerà l’anima tua.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
L’Eterno proteggerà il tuo uscire e il tuo entrare da ora in eterno.