< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
שיר למעלות אשא עיני אל ההרים מאין יבא עזרי׃
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
עזרי מעם יהוה עשה שמים וארץ׃
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
אל יתן למוט רגלך אל ינום שמרך׃
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
הנה לא ינום ולא יישן שומר ישראל׃
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
יהוה שמרך יהוה צלך על יד ימינך׃
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
יומם השמש לא יככה וירח בלילה׃
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
יהוה ישמרך מכל רע ישמר את נפשך׃
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
יהוה ישמר צאתך ובואך מעתה ועד עולם׃

< Zabura 121 >