< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
J’ai levé les yeux vers les montagnes, d’où me viendra le secours.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Mon secours vient du Seigneur, qui a fait le ciel et la terre.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Qu’il ne permette pas que ton pied soit ébranlé, et qu’il ne s’assoupisse pas, celui qui te garde.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Vois, il ne s’assoupira, ni ne dormira, celui qui garde Israël.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
C’est le Seigneur qui te garde, c’est le Seigneur qui est ta protection; il est sur ta main droite.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Pendant le jour, le soleil ne le brûlera pas, ni la lune pendant la nuit.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Le Seigneur te garde de tout mal; que le Seigneur garde ton âme.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Que le Seigneur garde ton entrée et ta sortie, dès ce moment et jusqu’à jamais.