< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Cantique de Maaloth. J'élève mes yeux vers les montagnes d'où me viendra le secours.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Mon secours vient de l'Éternel, qui a fait les cieux et la terre.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Il ne permettra pas que ton pied chancelle; celui qui te garde ne sommeillera point.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Voici, celui qui garde Israël ne sommeillera point, et ne s'endormira point.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
L'Éternel est celui qui te garde; l'Éternel est ton ombre; il est à ta main droite.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Le soleil ne te frappera point pendant le jour, ni la lune pendant la nuit.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
L'Éternel te gardera de tout mal; il gardera ton âme.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
L'Éternel gardera ta sortie et ton entrée, dès maintenant et à toujours.