< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Matkalaulu. Minä nostan silmäni vuoria kohti: mistä tulee minulle apu?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Apu minulle tulee Herralta, joka on tehnyt taivaan ja maan.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Hän ei salli sinun jalkasi horjua, sinun varjelijasi ei torku.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Katso, hän, joka Israelia varjelee, ei torku eikä nuku.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Herra on sinun varjelijasi, Herra on suojaava varjosi sinun oikealla puolellasi.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Ei polta sinua aurinko päivällä, eikä kuu yöllä.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Herra varjelee sinut kaikesta pahasta, hän varjelee sinun sielusi.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Herra varjelee sinun lähtemisesi ja tulemisesi, nyt ja iankaikkisesti.

< Zabura 121 >