< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
[When we travel toward Jerusalem], I look up toward the hills [and I ask myself], “Who will help me?”
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
[And my answer is] that Yahweh is the one who helps me; he is the one who made heaven and the earth.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
He will not allow us to fall/stumble; God, who protects us, will not fall asleep.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
The one who protects us Israeli people never gets sleepy, nor does he sleep [LIT].
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Yahweh watches over us; he is like the shade [MET] [that protects us from the sun].
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
[He will not allow] the sun to harm us during the day, and [he will not allow] the moon to harm us during the night.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Yahweh will protect us from being harmed in any manner; he will keep us safe.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
He will protect us from the time that we leave [our houses in the morning] until we return [in the evening]; he will protect us now, and he will protect us forever.

< Zabura 121 >