< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
A song of ascents. I lift up my eyes to the mountains. From where will help for me come?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
My help will come from the Lord the creator of heaven and earth.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Your foot he will not let stumble: he who guards you will not sleep.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
He who watches over Israel will neither slumber nor sleep.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
The Lord himself protects you, is your shelter beside you.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
The sun by day will not strike you, nor the moon by night.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
From all harm the Lord will guard you, will watch over your life.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
The Lord will guard your going and coming from now and for evermore.