< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
“A psalm of the steps, or the goings up.” I lift up mine eyes to the hills: Whence cometh my help?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
My help cometh from the LORD, Who made heaven and earth.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
He will not suffer thy foot to stumble; Thy guardian doth not slumber.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Behold, the guardian of Israel Doth neither slumber nor sleep.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
The LORD is thy guardian; The LORD is thy shade at thy right hand.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
The sun shall not smite thee by day, Nor the moon by night.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
The LORD will preserve thee from all evil; He will preserve thy life.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
The LORD will preserve thee, when thou goest out and when thou comest in, From this time forth for ever.

< Zabura 121 >