< Zabura 121 >
1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
I have lifted up my eyes to the mountains, from whence help shall come to me.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
My help is from the Lord, who made heaven and earth.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
May he not suffer thy foot to be moved: neither let him slumber that keepeth thee.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Behold he shall neither slumber nor sleep, that keepeth Israel.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
The Lord is thy keeper, the Lord is thy protection upon thy right hand.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
The sun shall not burn thee by day: nor the moon by night.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
The Lord keepeth thee from all evil: may the Lord keep thy soul.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
May the Lord keep thy going in and thy going out; from henceforth now and for ever.