< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Een bedevaartslied. Ik hef mijn ogen omhoog naar de bergen: "Vanwaar komt mijn hulp?"
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Mijn hulp komt van Jahweh, Die hemel en aarde heeft gemaakt!
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Neen, Hij laat uw voeten niet struikelen, Hij slaapt niet, uw Wachter;
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Neen, Hij sluimert noch dommelt, Israëls Beschermer!
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Jahweh is uw Behoeder, Uw schaduw aan uw rechterhand:
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Overdag zal de zon u niet hinderen, En de maan niet des nachts.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Jahweh behoedt u voor iedere ramp, Hij is bezorgd voor uw leven;
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Jahweh waakt over uw komen en gaan Van nu af tot in eeuwigheid.

< Zabura 121 >