< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
(Sang til Festrejserne.) Jeg løfter mine Øjne til Bjergene: Hvorfra kommer min Hjælp?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Fra HERREN kommer min Hjælp, fra Himlens og Jordens Skaber.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Din fod vil han ej lade vakle, ej blunder han, som bevarer dig;
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
nej, han blunder og sover ikke, han, som bevarer Israel.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
HERREN er den, som bevarer dig, HERREN er din Skygge ved din højre;
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Solen stikker dig ikke om Dagen, og Månen ikke om Natten;
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
HERREN bevarer dig mod alt ondt, han bevarer din Sjæl;
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
HERREN bevarer din Udgang og Indgang fra nu og til evig Tid!

< Zabura 121 >