< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Hac ilahisi Sıkıntıya düşünce RAB'be seslendim; Yanıtladı beni.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Ya RAB, kurtar canımı yalancı dudaklardan, Aldatıcı dillerden!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Ey aldatıcı dil, RAB ne verecek sana, Daha ne verecek?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Yiğidin sivri oklarıyla Retem çalısından alevli korlar!
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Vay bana, Meşek'te garip kaldım sanki, Kedar çadırları arasında oturdum.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Fazla kaldım Barıştan nefret edenler arasında.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Ben barış yanlısıyım, Ama söze başladığımda, Onlar savaşa kalkıyor!