< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Sa aking kahirapan ay dumaing ako sa Panginoon, at sinagot niya ako.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Iligtas mo ang aking kaluluwa, Oh Panginoon, sa mga sinungaling na labi, at mula sa magdarayang dila.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Anong maibibigay sa iyo, at anong magagawa pa sa iyo, ikaw na magdarayang dila?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Mga hasang pana ng makapangyarihan, at mga baga ng enebro.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Sa aba ko, na nakikipamayan sa Mesech, na tumatahan ako sa mga tolda sa Kedar!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Malaon ng tinatahanan ng aking kaluluwa na kasama niyang nagtatanim sa kapayapaan.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Ako'y sa kapayapaan: nguni't pagka ako'y nagsasalita, sila'y sa pakikidigma.

< Zabura 120 >