< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
En visa i högre choren. Jag ropar till Herran i mine nöd, och han bönhörer mig.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Herre, fräls mina själ ifrå lögnaktiga munnar, och ifrå falska tungo.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Hvad kan den falska tungan göra dig? Och hvad kan hon uträtta?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Hon är såsom ens väldigs skarpe pilar, såsom eld i enebärsträ.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Ve mig, att jag en främling är ibland Mesech; jag måste bo ibland Kedars hyddor.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Det varder mine själ långt att bo när dem, som friden hata.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Jag håller frid; men när jag talar, så taga de till att örliga.