< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Cántico gradual. A JEHOVÁ llamé estando en angustia, y él me respondió.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Libra mi alma, oh Jehová, de labio mentiroso, de la lengua fraudulenta.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
¿Qué te dará, ó qué te aprovechará, oh lengua engañosa?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Agudas saetas de valiente, con brasas de enebro.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
¡Ay de mí, que peregrino en Mesech, [y] habito entre las tiendas de Kedar!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Mucho se detiene mi alma con los que aborrecen la paz.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Yo soy pacífico: mas ellos, así que hablo, [me] hacen guerra.