< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Cântico dos degraus: Em minha angústia clamei ao SENHOR, e ele me respondeu.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Ó SENHOR, livra minha alma dos lábios mentirosos, da língua enganadora.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
O que ele te dará, e o que ele fará contigo, ó língua enganadora?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Flechas afiadas de um guerreiro, com brasas de zimbro.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Ai de mim, que peregrino em Meseque, [e] habito nas tendas de Quedar!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Minha alma morou [tempo] demais com os que odeiam a paz.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Eu sou da paz; mas quando falo, eles [entram] em guerra.

< Zabura 120 >