< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
En sang ved festreisene. Til Herren ropte jeg i min nød, og han svarte mig.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Herre, fri min sjel fra en løgnaktig lebe, fra en falsk tunge!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Hvad vil han gi dig, og hvad mere vil han gi dig, du falske tunge?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Voldsmannens skarpe piler og glør av gyvelbusken.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Ve mig, at jeg lever som fremmed iblandt Mesek, at jeg bor ved Kedars telt!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Lenge nok har min sjel bodd hos dem som hater fred.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Jeg er bare fred, men når jeg taler, er de ferdige til krig.

< Zabura 120 >