< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
canticum graduum ad Dominum cum tribularer clamavi et exaudivit me
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Domine libera animam meam a labiis iniquis a lingua dolosa
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
quid detur tibi et quid adponatur tibi ad linguam dolosam
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
sagittae potentis acutae cum carbonibus desolatoriis
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
heu mihi quia incolatus meus prolongatus est habitavi cum habitationibus Cedar
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
multum incola fuit anima mea
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
cum his qui oderant pacem eram pacificus cum loquebar illis inpugnabant me gratis