< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
[Ein Stufenlied.] Zu Jehova rief ich in meiner Bedrängnis, und er erhörte mich.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Jehova, errette meine Seele von der Lippe der Lüge, von der Zunge des Truges!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Was soll man [O. er [Gott]] dir geben und was dir hinzufügen, du Zunge des Truges?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Scharfe Pfeile eines Gewaltigen, samt glühenden Kohlen der Ginster.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Wehe mir, daß ich weile in Mesech, daß ich wohne bei den Zelten Kedars!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Lange [O. Genug] hat meine Seele bei denen gewohnt, die den Frieden hassen.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Ich will nur Frieden; [W. Ich bin Friede] aber wenn ich rede, so sind sie für Krieg.