< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Cantique de Maaloth. J'ai crié à l'Éternel dans ma détresse, et il m'a exaucé.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Éternel, délivre mon âme des lèvres menteuses, de la langue qui trompe!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Que te donnera, que te rapportera la langue trompeuse?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Des flèches aiguës comme celles du guerrier, avec les charbons ardents du genêt.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Malheureux que je suis de séjourner en Méshec, de demeurer parmi les tentes de Kédar!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Trop longtemps mon âme a demeuré avec celui qui hait la paix.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Je veux la paix; mais dès que je parle, ils sont pour la guerre.

< Zabura 120 >