< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
A song of ascents. In my distress I called out to Yahweh, and he answered me.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Rescue my life, Yahweh, from those who lie with their lips and deceive with their tongues.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
How will he punish you, and what more will he do to you, you who have a lying tongue?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
He will punish you with the arrows of a warrior sharpened over burning coals of the broom tree.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Woe is me because I temporarily live in Meshech; I lived previously among the tents of Kedar.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
For too long I have lived with those who hate peace.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
I am for peace, but when I speak, they are for war.

< Zabura 120 >