< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
[the] song of The ascents to Yahweh in distress of me I called out and he answered me.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
O Yahweh deliver! self my from a lip of falsehood from a tongue deceit.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
What? will anyone give to you and what? will anyone add to you O tongue deceit.
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Arrows of a warrior sharpened with burning coals of broom plants.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Woe! to me that I have sojourned Meshech I have dwelt with [the] tents of Kedar.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Much it has dwelt itself self my with [one who] hates peace.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
I [am] peace and that I speak they [are] for war.

< Zabura 120 >