< Zabura 120 >
1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
A song of ascents. In distress I cried to the Lord, and he answered me.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
“Deliver me, Lord, from the lip that is false and the tongue that is crafty.”
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
What shall he give to you, you tongue that is crafty? What yet shall he give to you?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Arrows of warrior, sharpened, with glowing broom coals together.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Woe is me that I sojourn in Meshech, that I live by the tents of Kedar.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Already too long have I dwelt among those who hate peace.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
I am for peace: but when I speak of it, they are for war.