< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
A Song of the going up. In my trouble my cry went up to the Lord, and he gave me an answer.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
O Lord, be the saviour of my soul from false lips, and from the tongue of deceit.
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
What punishment will he give you? what more will he do to you, you false tongue?
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Sharp arrows of the strong, and burning fire.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Sorrow is mine because I am strange in Meshech, and living in the tents of Kedar.
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
My soul has long been living with the haters of peace.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
I am for peace: but when I say so, they are for war.

< Zabura 120 >