< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
(Sang til Festrejserne.) Jeg råbte til HERREN i Nød, og han svarede mig.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
HERRE, udfri min Sjæl fra Løgnelæber, fra den falske Tunge!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Der ramme dig dette og hint, du falske Tunge!
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
Den stærkes Pile er hvæsset ved glødende Gyvel.
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Ve mig, at jeg må leve som fremmed i Mesjek, bo iblandt Kedars Telte!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Min Sjæl har længe nok boet blandt Folk, som hader Fred.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Jeg vil Fred; men taler jeg, vil de Krig!

< Zabura 120 >