< Zabura 12 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Müzik şefi için - Sekiz telli sazlarla - Davut'un mezmuru Kurtar beni, ya RAB, sadık kulun kalmadı, Güvenilir insanlar yok oldu.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Herkes birbirine yalan söylüyor, Dalkavukluk, ikiyüzlülük ediyor.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
Sustursun RAB dalkavukların ağzını, Büyüklenen dilleri.
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
Onlar ki, “Dilimizle kazanırız, Dudaklarımız emrimizde, Kim bize efendilik edebilir?” derler.
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
“Şimdi kalkacağım” diyor RAB, “Çünkü mazlumlar eziliyor, Yoksullar inliyor, Özledikleri kurtuluşu vereceğim onlara.”
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
RAB'bin sözleri pak sözlerdir; Toprak ocakta eritilmiş, Yedi kez arıtılmış gümüşe benzer.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Sen onları koru, ya RAB, Bu kötü kuşaktan hep uzak tut!
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
İnsanlar arasında alçaklık rağbet görünce, Kötüler her yanda dolaşır oldu.

< Zabura 12 >