< Zabura 12 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Til sangmesteren, efter Sjeminit; en salme av David. Frels, Herre! for de fromme er borte, de trofaste er forsvunnet blandt menneskenes barn.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Løgn taler de, hver med sin næste, med falske leber; med tvesinnet hjerte taler de.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
Herren utrydde alle falske leber, den tunge som taler store ord,
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
dem som sier: Ved vår tunge skal vi få overhånd, våre leber er med oss, hvem er herre over oss?
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
For de elendiges ødeleggelses skyld, for de fattiges sukks skyld vil jeg nu reise mig, sier Herren; jeg vil gi dem frelse som stunder efter den.
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
Herrens ord er rene ord, likesom sølv som er renset i en smeltedigel i jorden, syv ganger renset.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Du, Herre, vil bevare dem, du vil vokte dem for denne slekt evindelig.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
Rundt omkring svermer de ugudelige, når skarn er ophøiet blandt menneskenes barn.

< Zabura 12 >