< Zabura 12 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Siza, Nkosi, ngoba owesaba uNkulunkulu kasekho, ngoba abathembekileyo banyamalele basuka ebantwaneni babantu.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Bakhuluma okuyize, ngulowo lalowo lomakhelwane wakhe; indebe ezilalisayo, bakhuluma nganhliziyombili.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
INkosi izaquma zonke indebe ezilalisayo, ulimi olukhuluma izinto zokuzidla;
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
abathi: Sizanqoba ngolimi lwethu, indebe zethu ngezethu; ngubani oyinkosi phezu kwethu?
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
Ngenxa yokubandezelwa kwabayanga, ngenxa yokububula kwabaswelayo, sengizavuka, kutsho iNkosi. Ngizabeka ekulondolozekeni amvuthelayo.
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
Amazwi eNkosi angamazwi ahlambulukileyo, isiliva esizanywe esithandweni senhlabathi, sihlanjululwe kasikhombisa.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Wena, Nkosi, uzabagcina, ubavikele kulesisizukulwana kuze kube nininini.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
Ababi bayahambahamba inhlangothi zonke, lapho amanyala ephakanyiswa phakathi kwabantwana babantu.