< Zabura 12 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Psaume de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Seminith. Délivre, ô Eternel! parce que l'homme de bien ne se voit plus, [et] que les véritables ont disparu entre les fils des hommes.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Chacun dit la fausseté à son compagnon avec des lèvres flatteuses, et ils parlent avec un cœur double.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
L'Eternel veuille retrancher toutes les lèvres flatteuses, [et] la langue qui parle fièrement.
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
Parce qu'ils disent: nous aurons le dessus par nos langues; nos lèvres sont en notre puissance; qui sera Seigneur sur nous?
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
A cause du mauvais traitement que l'on fait aux affligés, à cause du gémissement des pauvres, je me lèverai maintenant, dit l'Eternel, je mettrai en sûreté celui à qui l'on tend des pièges.
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
Les paroles de l'Eternel sont des paroles pures, c'est un argent affiné au fourneau de terre, épuré par sept fois.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Toi, Eternel! gardes-les, [et] préserve à jamais chacun d'eux de cette race de gens.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
[Car] les méchants se promènent de toutes parts, tandis que des gens abjects sont élevés entre les fils des hommes.

< Zabura 12 >