< Zabura 12 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Veisuunjohtajalle; matalassa äänialassa; Daavidin virsi. Auta, Herra, sillä hurskaat ovat hävinneet, uskolliset ovat kadonneet ihmislasten joukosta.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
He puhuvat valhetta toinen toisellensa, puhuvat liukkain huulin, kaksimielisin sydämin.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
Hävittäköön Herra kaikki liukkaat huulet, kielen, joka kerskuen puhuu,
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
ne, jotka sanovat: "Kielemme voimalla me olemme väkevät; huulemme ovat meidän tukemme; kuka on meille herra?"
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
"Kurjien sorron tähden, köyhien huokausten tähden minä nyt nousen", sanoo Herra, "tuon pelastuksen sille, joka sitä huoaten ikävöitsee".
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
Herran sanat ovat selkeitä sanoja, hopeata, joka kirkkaana valuu sulattimesta maahan, seitsenkertaisesti puhdistettua.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Sinä, Herra, varjelet heitä, suojelet hänet iäti tältä sukukunnalta.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
Yltympäri jumalattomat rehentelevät, kun kataluus pääsee valtaan ihmislasten seassa.