< Zabura 12 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
To the Chief Musician. On the Octave. A Melody of David. O save Yahweh, for the man of lovingkindness, is no more, for the faithful, have vanished, from among the sons of men.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Deception, speak they, every one with his neighbour, —with lips uttering smooth things—with a heart and a heart, do they speak.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
May Yahweh cut off All the lips that utter smooth things, —the tongue that speaketh swelling words;
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
Them who say—With our tongue, will we prevail, our lips, are our own, who is our master?
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
Because of violence done to the poor, because of the crying of the needy, Now, will I arise! O may Yahweh say, —I will place [him] in safety—let him puff at him!
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
The words of Yahweh, are words, that are pure, silver refined in a crucible of earth, purified seven times!
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Thou, O Yahweh, wilt keep them, —Thou wilt guard him, from this generation unto times age-abiding.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
On every side, the lawless, march about, —when worthlessness is exalted by the sons of men.

< Zabura 12 >