< Zabura 12 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
Kuom jatend wer. Kaluwore gi sheminith. Zaburi mar Daudi. Kony ji yaye Jehova Nyasaye, nikech joma oluoro Nyasaye koro onge; joma jo-adiera oserumo e dier ji.
2 Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
Ngʼato ka ngʼato riambo ne nyawadgi; dhogi mohero jaro ji wuoyo gi wuond.
3 Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
Mad Jehova Nyasaye ongʼad oko lep duto ma jaro ji kod lep duto masungore;
4 masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
mawacho niya, “Wabiro wuoyo kaka wahero; kendo onge ngʼama biro tamowa. Koso en ngʼa ma ruodhwa manyalo tamowa timo kamano?”
5 “Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
“Nikech dich modigo joma ok nyal kod chur ma joma ochando churgo, koro abiro aa malo,” Jehova Nyasaye owacho. “Abiro ritogi e lwet joma sandogi.”
6 Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
Weche Jehova Nyasaye liw, giliw ka fedha moleny e lowo mowangʼ maliet ha, mopwodhi ndalo abiriyo.
7 Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
Yaye Jehova Nyasaye, yie iritwa maber kik gimoro ohinywa kendo reswa e lwet joma kamago nyaka chiengʼ.
8 Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.
Joma timbegi richo wuotho koni gi koni kendo gima rach ema ji puoyo.

< Zabura 12 >