< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Heri wale walio waadilifu katika njia zao, wanaoenenda katika sheria ya Bwana.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Heri wale wanaozishika shuhuda zake, wamtafutao kwa moyo wao wote.
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Wasiofanya lolote lililo baya, wanaoenenda katika njia zake.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Umetoa maagizo yako ili tuyatii kwa ukamilifu.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Laiti mwenendo wangu ungekuwa imara katika kuyatii maagizo yako!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Hivyo mimi sitaaibishwa ninapozingatia amri zako zote.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Nitakusifu kwa moyo mnyofu ninapojifunza sheria zako za haki.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Nitayatii maagizo yako; usiniache kabisa.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Kijana aifanye njia yake kuwa safi jinsi gani? Ni kwa kutii, akilifuata neno lako.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Ninakutafuta kwa moyo wangu wote, usiniache niende mbali na amri zako.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Nimelificha neno lako moyoni mwangu ili nisikutende dhambi.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Sifa ni zako, Ee Bwana, nifundishe maagizo yako.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Kwa midomo yangu nitasimulia sheria zote zinazotoka katika kinywa chako.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Ninafurahia kufuata sheria zako kama mtu afurahiaye mali nyingi.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Ninatafakari maagizo yako na kuziangalia njia zako.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Ninafurahia maagizo yako, wala sitalipuuza neno lako.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Mtendee mema mtumishi wako, nami nitaishi; nitalitii neno lako.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Yafungue macho yangu nipate kuona mambo ya ajabu katika sheria yako.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Mimi ni mgeni duniani, usinifiche amri zako.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Nafsi yangu inataabika kwa shauku kubwa juu ya sheria zako wakati wote.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Unawakemea wenye majivuno, waliolaaniwa waendao mbali na amri zako.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Niondolee dharau na dhihaka, kwa kuwa ninazishika sheria zako.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Ingawa watawala huketi pamoja na kunisingizia, mtumishi wako atatafakari juu ya maagizo yako.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Sheria zako ni furaha yangu, nazo ni washauri wangu.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Nimelazwa chini mavumbini, yahifadhi maisha yangu sawasawa na neno lako.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Nilikueleza njia zangu ukanijibu, nifundishe sheria zako.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Nijulishe mafundisho ya mausia yako, nami nitatafakari maajabu yako.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Nafsi yangu imechakazwa kwa huzuni, uniimarishe sawasawa na neno lako.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Niepushe na njia za udanganyifu, kwa neema unifundishe sheria zako.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
Nimechagua njia ya kweli, nimekaza moyo wangu katika sheria zako.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Nimengʼangʼania sheria zako, Ee Bwana, usiniache niaibishwe.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Nakimbilia katika njia ya maagizo yako, kwa kuwa umeuweka moyo wangu huru.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Ee Bwana, nifundishe kuyafuata maagizo yako, nami nitayashika mpaka mwisho.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Nipe ufahamu, nami nitaishika sheria yako na kuitii kwa moyo wangu wote.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Niongoze kwenye njia ya amri zako, kwa kuwa huko napata furaha.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Ugeuze moyo wangu kuelekea sheria zako, na siyo kwenye mambo ya ubinafsi.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Geuza macho yangu kutoka kwenye mambo yasiyofaa, uyahifadhi maisha yangu sawasawa na neno lako.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Mtimizie mtumishi wako ahadi yako, ili upate kuogopwa.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Niondolee aibu ninayoiogopa, kwa kuwa sheria zako ni njema.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Tazama jinsi ninavyoonea shauku mausia yako! Hifadhi maisha yangu katika haki yako.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Ee Bwana, upendo wako usiokoma unijie, wokovu wako sawasawa na ahadi yako,
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
ndipo nitakapomjibu anayenidhihaki, kwa kuwa ninalitumainia neno lako.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Usilinyakue neno la kweli kutoka kinywani mwangu, kwa kuwa nimeweka tumaini langu katika amri zako.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Nitaitii amri yako daima, naam, milele na milele.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Nitatembea nikiwa huru, kwa kuwa nimejifunza mausia yako.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Nitasema sheria zako mbele za wafalme wala sitaaibishwa,
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
kwa kuwa ninazifurahia amri zako kwa sababu ninazipenda.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Ninaziinulia amri zako ambazo ninazipenda mikono yangu, nami ninatafakari juu ya maagizo yako.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Kumbuka neno lako kwa mtumishi wako, kwa sababu umenipa tumaini.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Faraja yangu katika mateso yangu ni hii: Ahadi yako inahifadhi maisha yangu.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Wenye majivuno wamenisimanga bila kuchoka, hata hivyo sitaiacha sheria yako.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Ee Bwana, ninazikumbuka sheria zako za zamani, nazo zinanifariji.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Nimeshikwa sana na ghadhabu kwa ajili ya waovu, ambao wameacha sheria yako.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Maagizo yako ni kiini cha nyimbo zangu popote ninapoishi.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Ee Bwana, wakati wa usiku ninalikumbuka jina lako, nami nitatii sheria yako.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Hili limekuwa zoezi langu: nami ninayatii mausia yako.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Ee Bwana, wewe ni fungu langu, nimeahidi kuyatii maneno yako.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Nimetafuta uso wako kwa moyo wangu wote, nihurumie sawasawa na ahadi yako.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
Nimezifikiri njia zangu na nimeelekeza hatua zangu katika mausia yako.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Nitafanya haraka bila kuchelewa kuzitii amri zako.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Hata waovu wanifunge kwa kamba, sitasahau sheria yako.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Usiku wa manane ninaamka kukushukuru kwa sababu ya sheria zako za haki.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Mimi ni rafiki kwa wale wote wakuchao, kwa wote wanaofuata mausia yako.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Ee Bwana, dunia imejaa upendo wako, nifundishe maagizo yako.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Mtendee wema mtumishi wako Ee Bwana, sawasawa na neno lako.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Nifundishe maarifa na uamuzi mzuri, kwa kuwa ninaamini amri zako.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Kabla sijapata shida nilipotea njia, lakini sasa ninalitii neno lako.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Wewe ni mwema, unalotenda ni jema, nifundishe maagizo yako.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Ingawa wenye majivuno wamenisingizia uongo, nitafuata mausia yako kwa moyo wangu wote.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Mioyo yao ni katili na migumu, bali mimi napendezwa na sheria yako.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Ilikuwa vyema mimi kupata shida ili nipate kujifunza maagizo yako.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Sheria inayotoka kinywani mwako ina thamani kubwa kwangu kuliko maelfu ya vipande vya fedha na dhahabu.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Mikono yako ilinifanya na kuniumba, nipe ufahamu niweze kujifunza amri zako.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Wakuchao wafurahie wanaponiona, kwa kuwa nimeweka tumaini langu katika neno lako.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Ee Bwana, ninajua kwamba sheria zako ni za haki, katika uaminifu wako umeniadhibu.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Upendo wako usiokoma uwe faraja yangu, sawasawa na ahadi yako kwa mtumishi wako.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Huruma yako na inijie ili nipate kuishi, kwa kuwa naifurahia sheria yako.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Wenye majivuno na waaibishwe kwa kunikosea mimi bila sababu, lakini mimi nitatafakari juu ya mausia yako.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Wale wakuchao na wanigeukie mimi, hao ambao wanazielewa sheria zako.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Moyo wangu usiwe na lawama katika kutii maagizo yako, ili nisiaibishwe.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Nafsi yangu inazimia kwa kutamani wokovu wako, lakini nimeweka tumaini langu katika neno lako.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Macho yangu yamefifia, nikingoja ahadi yako; ninasema, “Utanifajiri lini?”
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Ingawa nimekuwa kama kiriba kwenye moshi, bado sijasahau maagizo yako.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Mtumishi wako itampasa angoje mpaka lini? Ni lini utawaadhibu washtaki wangu?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Wenye majivuno wananichimbia mashimo, kinyume na sheria yako.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Amri zako zote ni za kuaminika; unisaidie, kwa sababu watu wananishtaki bila sababu.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Walikaribia kabisa kunifuta kutoka uso wa dunia, lakini sijaacha mausia yako.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Yahifadhi maisha yangu sawasawa na upendo wako, nami nitatii sheria za kinywa chako.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Ee Bwana, neno lako ni la milele, linasimama imara mbinguni.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Uaminifu wako unaendelea kwa vizazi vyote, umeiumba dunia, nayo inadumu.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Sheria zako zinadumu hadi leo, kwa kuwa vitu vyote vinakutumikia.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Kama nisingefurahia sheria yako, ningeangamia katika taabu zangu.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Sitasahau mausia yako kamwe, kwa maana kwayo umehifadhi maisha yangu.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Uniokoe, kwa maana mimi ni wako, kwa kuwa nimetafuta mausia yako.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Waovu wanangojea kuniangamiza, bali mimi ninatafakari sheria zako.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
Katika ukamilifu wote ninaona mna kikomo, lakini amri zako hazina mpaka.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Aha! Tazama, sheria yako naipenda mno ajabu. Ninaitafakari mchana kutwa.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Amri zako zimenipa hekima zaidi kuliko adui zangu, kwa kuwa nimezishika daima.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Nina akili zaidi kuliko walimu wangu wote, kwa kuwa ninatafakari juu ya sheria zako.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Nina ufahamu zaidi kuliko wazee, kwa kuwa ninayatii mausia yako.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
Nimezuia miguu yangu isiende kwenye kila njia mbaya, ili niweze kutii neno lako.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Sijaziacha sheria zako, kwa kuwa umenifundisha wewe mwenyewe.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Tazama jinsi maneno yako yalivyo matamu kwangu, matamu kuliko asali katika kinywa changu!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Ninapata ufahamu kutoka mausia yako, kwa hiyo ninachukia kila njia ya upotovu.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Neno lako ni taa ya miguu yangu na mwanga katika njia yangu.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
Nimeapa na nimethibitisha, kwamba nitafuata sheria zako za haki.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Nimeteseka sana, uhifadhi maisha yangu, Ee Bwana, sawasawa na neno lako.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Ee Bwana, pokea sifa za hiari za kinywa changu, nifundishe sheria zako.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Ingawa maisha yangu yako hatarini siku zote, sitasahau sheria yako.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Waovu wamenitegea mtego, lakini sijayakiuka maagizo yako.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Sheria zako ni urithi wangu milele, naam ni furaha ya moyo wangu.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Nimekusudia moyoni mwangu kuyafuata maagizo yako mpaka mwisho.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Ninachukia watu wa nia mbili, lakini ninapenda sheria yako.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Wewe ni kimbilio langu na ngao yangu, nimeweka tumaini langu katika neno lako.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Ondokeni kwangu, ninyi mtendao mabaya, ili niweze kushika amri za Mungu wangu!
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Nihifadhi sawasawa na ahadi yako, nami nitaishi; usiache matumaini yangu yakavunjwa.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Nitegemeze, nami nitaokolewa, nami daima nitayaheshimu maagizo yako.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Unawakataa wote wanaoyaasi maagizo yako, kwa maana udanganyifu wao ni bure.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Waovu wa nchi unawatupa kama takataka, kwa hivyo nazipenda sheria zako.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Mwili wangu unatetemeka kwa kukuogopa wewe, ninaziogopa sheria zako.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
Nimetenda yaliyo haki na sawa, usiniache mikononi mwa watesi wangu.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Mhakikishie mtumishi wako usalama, usiache wenye kiburi wanionee.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Macho yangu yamefifia, yakitazamia wokovu wako, na kuitazamia ahadi yako ya kweli.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Mfanyie mtumishi wako kulingana na upendo wako na unifundishe maagizo yako.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Mimi ni mtumishi wako; nipe ufahamu ili niweze kuelewa sheria zako.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Ee Bwana, wakati wako wa kutenda umewadia, kwa kuwa sheria yako inavunjwa.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Kwa sababu nazipenda amri zako zaidi ya dhahabu, naam, zaidi ya dhahabu safi,
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
na kwa sababu naona maagizo yako yote ni adili, nachukia kila njia potovu.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Sheria zako ni za ajabu, hivyo ninazitii.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Kuingia kwa maneno yako kunaleta nuru, kunampa mjinga ufahamu.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Nimefungua kinywa changu na kuhema, nikitamani amri zako.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Nigeukie na unihurumie, kama uwafanyiavyo siku zote wale wanaolipenda jina lako.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Ongoza hatua zangu kulingana na neno lako, usiache dhambi yoyote initawale.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Niokoe na uonevu wa wanadamu, ili niweze kutii mausia yako.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Mwangazie mtumishi wako uso wako na unifundishe amri zako.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Chemchemi za machozi zinatiririka kutoka machoni yangu, kwa kuwa sheria yako haifuatwi.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Ee Bwana, wewe ni mwenye haki, sheria zako ni sahihi.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Sheria ulizoziweka ni za haki, ni za kuaminika kikamilifu.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Jitihada yangu imenidhoofisha, kwa kuwa adui zangu wanayapuuza maneno yako.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ahadi zako zimejaribiwa kikamilifu, mtumishi wako anazipenda.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Ingawa ni mdogo na ninadharauliwa, sisahau mausia yako.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Haki yako ni ya milele, na sheria yako ni kweli.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Shida na dhiki zimenipata, lakini amri zako ni furaha yangu.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Sheria zako ni sahihi milele, hunipa ufahamu ili nipate kuishi.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Ee Bwana, ninakuita kwa moyo wangu wote, nami nitayatii maagizo yako.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Ninakuita; niokoe nami nitazishika sheria zako.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Ninaamka asubuhi na mapema na kukuomba msaada; nimeweka tumaini langu katika neno lako.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Sikufumba macho yangu usiku kucha, ili niweze kutafakari juu ya ahadi zako.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Usikie sauti yangu sawasawa na upendo wako, Ee Bwana, uyahifadhi maisha yangu, sawasawa na sheria zako.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Wale wanaopanga mipango miovu wako karibu nami, lakini wako mbali na sheria yako.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Ee Bwana, hata hivyo wewe u karibu, na amri zako zote ni za kweli.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Tangu zamani nimejifunza kutoka shuhuda zako kwamba umezithibitisha ili zidumu milele.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Yaangalie mateso yangu, uniokoe, kwa kuwa sijasahau sheria yako.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Nitetee katika hali hii yangu na unikomboe, uyahifadhi maisha yangu sawasawa na ahadi yako.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Wokovu uko mbali na waovu, kwa kuwa hawatafuti maagizo yako.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Ee Bwana, huruma zako ni kuu, uyahifadhi maisha yangu sawasawa na sheria zako.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Adui wanaonitesa ni wengi, lakini mimi sitaziacha sheria zako.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Ninawatazama wasioamini kwa chuki, kwa kuwa hawalitii neno lako.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Tazama jinsi ninavyopenda mausia yako; Ee Bwana, uyahifadhi maisha yangu, sawasawa na upendo wako.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Maneno yako yote ni kweli, sheria zako zote za haki ni za milele.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Watawala wamenitesa bila sababu, lakini moyo wangu unatetemeka kwa neno lako.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Nafurahia ahadi zako kama mtu aliyepata mateka mengi.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Ninachukia na kuchukizwa sana na uongo, lakini napenda sheria yako.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Ninakusifu mara saba kwa siku, kwa ajili ya sheria zako za haki.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Wanaopenda sheria yako wana amani tele, wala hakuna kitu kinachoweza kuwakwaza.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Ee Bwana, ninangojea wokovu wako, nami ninafuata amri zako,
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Ninazitii sheria zako, kwa sababu ninazipenda mno.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
Nimetii mausia yako na sheria zako, kwa kuwa njia zangu zote zinajulikana kwako.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Ee Bwana, kilio changu na kifike mbele zako, nipe ufahamu sawasawa na neno lako.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Maombi yangu na yafike mbele zako, niokoe sawasawa na ahadi yako.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Midomo yangu na ibubujike sifa, kwa kuwa unanifundisha maagizo yako.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Ulimi wangu na uimbe kuhusu neno lako, kwa kuwa amri zako zote ni za haki.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Mkono wako uwe tayari kunisaidia, kwa kuwa nimechagua mausia yako.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Ee Bwana, ninatamani wokovu wako, na sheria yako ni furaha yangu.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Nijalie kuishi ili nipate kukusifu, na sheria zako zinitegemeze.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Nimetangatanga kama kondoo aliyepotea. Mtafute mtumishi wako, kwa kuwa sijasahau amri zako.

< Zabura 119 >