< Zabura 119 >
1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Inmensamente felices son los de proceder intachable, Quienes andan en la Ley de Yavé.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Inmensamente felices son los que observan sus Testimonios, Los que lo buscan de todo corazón.
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Ellos tampoco cometen injusticia. Andan en los caminos de Él.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Tú nos ordenaste Que guardemos tus Preceptos con diligencia.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
¡Cómo anhelo que sean establecidos mis caminos, Para guardar tus Estatutos!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Entonces no sería yo avergonzado Cuando observe todos tus Mandamientos.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Te daré gracias con rectitud de corazón Cuando aprenda tus rectos juicios.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Guardaré tus Estatutos. No me abandones completamente.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
¿Cómo puede un joven guardar puro su camino? Al mantenerlo según tu Palabra.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Con todo mi corazón te he buscado. No permitas que me desvíe de tus Mandamientos.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Tu Palabra atesoré en mi corazón Para no pecar contra Ti.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Bendito seas Tú, oh Yavé. Enséñame tus Estatutos.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Con mis labios conté Todas las Ordenanzas de tu boca.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Me he regocijado en el camino de tus Testimonios, Tanto como en todas [las] riquezas.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Meditaré en tus Ordenanzas. Consideraré tus caminos.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Me deleitaré en tus Estatutos. No olvidaré tu Palabra.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Concede beneficio a tu esclavo, Que yo viva y guarde tu Palabra.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Abre mis ojos, Para que yo vea las maravillas de tu Ley.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Soy un peregrino en la tierra. No encubras de mí tus Mandamientos.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Mi alma se quebranta con el anhelo De seguir tus Ordenanzas en todo tiempo.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Tú reprendes a los arrogantes. Son malditos los que se desvían de tus Mandamientos.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Aparta de mí el oprobio y el menosprecio, Porque he guardado tus Testimonios.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Aunque los magistrados se sienten Y hablen contra mí, Tu esclavo medita en tus Estatutos.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Tus Testimonios son también mi deleite y mis consejeros.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Postrada en el polvo está mi alma. Dame vida según tu Palabra.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Te declaré mis caminos, Y me respondiste. Enséñame tus Estatutos.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Hazme entender la vía de tus Estatutos Para que yo medite en sus maravillas.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Mi vida se disuelve a causa de la tristeza. Fortaléceme según tu Palabra.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Aparta de mí el camino falso, Y con bondad concédeme tu Ley.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
Escogí el camino fiel. Me enfrenté a tus Ordenanzas.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Me apegué a tus Testimonios, oh Yavé. No me entregues a la vergüenza.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Correré por el camino de tus Mandamientos, Porque Tú ensancharás mi corazón.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Enséñame, oh Yavé, la vía de tus Estatutos, Y lo guardaré hasta el fin.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Dame entendimiento para que yo observe tu Ley, Y la observaré de todo corazón.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Hazme andar por la senda de sus Mandamientos, Porque en ella me deleito.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Inclina mi corazón a tus Testimonios, Y no a ganancia deshonesta.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Aparta mis ojos para que no miren vanidad. Revíveme en tus caminos.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Establece tu Palabra para tu esclavo, Como la que produce reverencia a Ti.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Aleja de mí la reprobación que temo, Porque tus Ordenanzas son buenas.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Mira, yo anhelo tus Preceptos. Revíveme en tu justicia.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Venga a mí, oh Yavé, tu misericordia, Tu salvación, conforme a tu Palabra,
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
A fin de que tenga respuesta para el que me reprueba, Porque confío en tu Palabra.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
No quites de mi boca en algún momento la Palabra de verdad, Porque yo confío en tus Ordenanzas.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Así observaré tu Ley continuamente, Eternamente y para siempre.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Andaré en libertad, Porque busco tus Preceptos.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Delante de reyes hablaré también de tus Testimonios, Y no me avergonzaré.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Me deleitaré en tus Mandamientos, Los cuales amo.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Alzaré mis manos hacia tus Mandamientos, Los cuales amo, Y meditaré en tus Estatutos.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Recuerda la promesa [dada] a tu esclavo, En la cual me ordenaste esperar.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Ella es mi consuelo en mi aflicción, Porque tu Palabra me da vida.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Muchos se burlan de mí, Pero no me apartan de tu Ley.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Recuerdo tus antiguas Ordenanzas, oh Yavé, Y me consuelo.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Indignación ardiente se apoderó de mí A causa de los perversos que abandonan tu Ley.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Tus Estatutos fueron cantos para mí En la casa de mi peregrinaje.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Recuerdo tu Nombre en la noche, oh Yavé, Y observo tu Ley.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Esto me sucedió Para que yo observe tus Preceptos.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Mi posesión es Yavé. Prometí que observaré tus Palabras.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Busqué tu favor con todo mi corazón. Sé bondadoso conmigo, según tu Palabra.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
Consideré mis caminos Y volví mis pies a tus Testimonios.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Me apresuré, no me demoré En guardar tus Mandamientos.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Las cuerdas de los perversos me rodearon, Pero no olvidé tu Ley.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
A medianoche me levanto Para darte gracias por tus justas Ordenanzas.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Soy compañero de todos los que te temen, Y de los que observan sus Preceptos.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Oh Yavé, la tierra está llena de tu misericordia. Enséñame tus Estatutos.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Oh Yavé, bien hiciste a tu esclavo según tu Palabra.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Enséñame buen discernimiento y conocimiento, Porque creo tus Mandamientos.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Antes de ser afligido me extravié, Pero ahora observo tu Palabra.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Bueno eres Tú Y haces lo bueno. Enséñame tus Estatutos.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Los arrogantes forjaron mentira contra mí. Yo observo tus Preceptos de todo corazón.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Los corazones de ellos están cubiertos de grasa. Yo me deleito en tu Ley.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Fue bueno para mí que fui afligido, Para que aprenda tus Estatutos.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Mejor me es la Ley de tu boca Que millares de oro y plata.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Tus manos me hicieron y me afirmaron. Dame entendimiento para que aprenda tus Mandamientos.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Que los que te reverencian Me vean y se alegren, Porque confié en tu Palabra.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Sé, oh Yavé, que tus juicios con justos, Y que me afligiste según tu fidelidad.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Oh, que tu misericordia me consuele, Conforme prometiste a tu esclavo.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Que tu compasión venga a mí, Para que yo viva, Porque tu Ley es mi deleite.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Sean avergonzados los arrogantes, Porque sin causa me calumnian, Pero yo meditaré en tus Preceptos.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Que se vuelvan a mí los que te temen, Los que conocen tus Testimonios.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Sea mi corazón íntegro en tus Estatutos, Para que no sea avergonzado.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Mi alma desfallece por tu salvación. Pero confío en tu Palabra.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Se consumen mis ojos [esperando] tu Palabra, Mientras digo: ¿Cuándo me consolará?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Aunque soy como odre en el humo, No olvido tus Estatutos.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
¿Cuántos son los días de tu esclavo? ¿Cuándo juzgarás a los que me persiguen?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Los arrogantes me cavaron fosa, Los que no concuerdan con tu Ley.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Todos tus Mandamientos son fieles. Me persiguen con engaño. Ayúdame.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Casi me destruyen en la tierra, Pero yo no abandono tus Preceptos.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Vivifícame según tu misericordia, Y observaré los Testimonios de tu boca.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Para siempre, oh Yavé, Tu Palabra permanece en el cielo.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Por todas las generaciones es tu fidelidad. Tú estableciste la tierra, y permanece.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Por tu mandato subsisten hasta hoy [todas las cosas], Porque todas ellas te sirven como esclavas.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Si tu Ley no fuera mi deleite, Entonces habría perecido en mi aflicción.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Jamás olvido tus Preceptos, Porque con ellos me vivificaste.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Tuyo soy. ¡Sálvame! Porque busqué tus Preceptos.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Me esperan los perversos para destruirme. Pero yo considero tus Testimonios.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
En toda perfección he visto límite. Tu Mandamiento es inmensamente amplio.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
¡Oh, cuánto amo yo tu Ley! Todo el día es mi meditación.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Tus Mandamientos me hacen más sabio que mis enemigos, Porque siempre están conmigo.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Tengo mejor entendimiento que todos mis maestros, Porque tus Testimonios son mi meditación.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Entiendo más que los ancianos, Porque observo tus Preceptos.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
De todo mal camino contuve mis pies, Para observar tu Palabra.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
No me aparté de tus Ordenanzas, Porque Tú mismo me enseñaste.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
¡Cuán dulces son tus Palabras a mi paladar, Más que miel a mi boca!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
De sus Preceptos recibo entendimiento, Por tanto aborrezco todo camino falso.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Lámpara a mis pies es tu Palabra, Y lumbrera a mi camino.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
Juré observar tus justas Ordenanzas. Lo cumpliré Y lo confirmo: Guardaré tus justas Ordenanzas.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Estoy afligido en gran manera. Oh Yavé, vivifícame según tu Palabra.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Acepta las ofrendas voluntarias de mi boca, oh Yavé, Y enséñame tus Ordenanzas.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Mi vida está de continuo en peligro, Pero yo no olvido tu Ley.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Los perversos me tienden una trampa, Pero yo no me desvío de tus Preceptos.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Tus Testimonios son mi herencia eterna, Porque ellos son el gozo de mi corazón.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Incliné mi corazón a cumplir tus Estatutos, De continuo hasta el fin.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Aborrezco a los de doble ánimo, Pero amo tu Ley.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Tú eres mi Refugio y mi Escudo. Confío en tu Palabra.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Apártense de mí, perversos, Para que yo observe los Mandamientos de mi ʼElohim.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Susténtame según tu Palabra para que viva Y no dejes que sea avergonzado de mi esperanza.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Susténtame para que sea salvo, Para que yo observe de continuo tus Estatutos.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Rechazas a todos los que se desvían de tus Estatutos, Porque su astucia es falsedad.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Removiste de la tierra [como] escoria a todos los perversos. Por tanto, amo tus Testimonios.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Mi carne se estremece de temor a Ti, Y ante tus juicios me lleno de pavor.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
Actué con justicia y rectitud. No me abandones a mis opresores.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Sé garante de tu esclavo para bien, Que no me opriman los arrogantes.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mis ojos desfallecen por tu salvación, Y por la Palabra de tu justicia.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Haz con tu esclavo según tu misericordia, Y enséñame tus Estatutos.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Yo soy tu esclavo. Dame entendimiento para comprender tus Testimonios.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Es tiempo de actuar, oh Yavé. Porque invalidaron tu Ley.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Por tanto amo tus Mandamientos Más que el oro, sí, más que el oro fino.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Por tanto estimo rectos todos tus Preceptos Con respecto a todas las cosas. Aborrezco todo camino falso.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
¡Maravillosos son tus Testimonios! Por tanto los observa mi alma.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
La exposición de tus Palabras alumbra. Da entendimiento a los simples.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Abrí bien mi boca y suspiré, Porque anhelaba tus Mandamientos.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Mírame y ten misericordia de mí, Como acostumbras con los que aman tu Nombre.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Afirma mis pasos con tu Palabra, Y no permitas que alguna iniquidad me domine.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Líbrame de la violencia de los hombres, Y observaré tus Mandamientos.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Haz resplandecer tu rostro sobre tu esclavo, Y enséñame tus Estatutos.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Manantiales de agua bajarán de mis ojos, Porque ellos no observan tu Ley.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Justo eres Tú, oh Yavé, Y rectos son tus juicios.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Tus Testimonios nos mandaste con justicia, Y extraordinaria fidelidad.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Mi celo me consume, Porque mis adversarios olvidaron tus Palabras.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Tu Palabra es muy pura, Por tanto, tu esclavo la ama.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Soy pequeño y despreciado, [Pero] no olvido tus Preceptos.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Tu justicia es eterna, Y tu Ley es verdad.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
La aflicción y la angustia me alcanzaron, [Pero] tus Mandamientos son mi delicia.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Tus Testimonios son justicia eterna. Dame entendimiento para que viva.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Clamo con todo mi corazón. Respóndeme, oh Yavé. Observaré tus Estatutos.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
A Ti clamo: ¡Sálvame! Y observaré tus Testimonios.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Me levanté antes del alba y clamé. Espero tu Palabra.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mis ojos se anticipan a las vigilias de la noche Para meditar en tu Palabra.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Oye mi voz según tu misericordia. Vivifícame, oh Yavé, según tus Ordenanzas.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Los que siguen la perversidad se acercan. Están lejos de tu Ley.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Tú, oh Yavé, estás cerca, Y todos tus Mandamientos son verdad.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Desde antaño conocí tus Testimonios, Que Tú estableciste para siempre.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Mira mi aflicción y rescátame, Porque yo no olvido tu Ley.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Defiende mi causa y redímeme, Vivifícame según tu Palabra.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Lejos de los perversos está la salvación, Porque no buscan tus Estatutos.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Oh Yavé, grandes son tus misericordias. Vivifícame según tus Ordenanzas.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Muchos son mis perseguidores y mis adversarios, [Pero] yo no me aparto de tus Testimonios.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Veo a los traidores y me disgusto, Porque ellos no observan tu Palabra.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Considera cuánto amo tus Preceptos. Vivifícame, oh Yavé, según tu misericordia.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
La suma de tu Palabra es verdad, Y eterna cada una de tus justas Ordenanzas.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Príncipes me persiguen sin causa, Pero mi corazón tiene temor a tus Palabras.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Me regocijo en tu Palabra Como el que halla gran despojo.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Aborrezco y repugno la mentira. Amo tu Ley.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Siete veces al día te alabo A causa de tus justas Ordenanzas.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Mucha paz tienen los que aman su Ley, Y no hay tropiezo para ellos.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Oh Yavé, espero tu salvación Y practico tus Mandamientos.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Mi alma observa tus Testimonios, Y los ama intensamente.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
Observo tus Preceptos y tus Testimonios, Porque todos mis caminos están delante de Ti.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Llegue mi clamor ante Ti, oh Yavé. Dame entendimiento según tu Palabra.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Llegue mi súplica ante Ti. Líbrame según tu Palabra.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mis labios rebozan alabanza Cuando Tú me enseñas tus Estatutos.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Hablará mi lengua tu Palabra, Porque todos tus Mandamientos son justicia.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Esté tu mano lista para socorrerme, Porque escogí tus Ordenanzas.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Anhelo tu salvación, oh Yavé, Y tu Ley es mi deleite.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Viva mi alma y te alabe, Y que me ayuden tus Ordenanzas.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Anduve errante como oveja perdida. Busca a tu esclavo, Porque no olvido tus Mandamientos.