< Zabura 119 >
1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Salige er de hvis vei er ulastelig, som vandrer i Herrens lov.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Salige er de som tar vare på hans vidnesbyrd, som søker ham av hele sitt hjerte
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
og ikke gjør urett, men vandrer på hans veier.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Du har gitt dine befalinger forat en skal holde dem nøie.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
O, at mine veier måtte bli faste, så jeg holder dine forskrifter!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Da skal jeg ikke bli til skamme når jeg gir akt på alle dine bud.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Jeg vil prise dig i hjertets opriktighet når jeg lærer din rettferdighets lover å kjenne.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Dine forskrifter vil jeg holde; du må ikke rent forlate mig!
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Hvorved skal den unge holde sin sti ren? Ved å holde sig efter ditt ord.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Av hele mitt hjerte har jeg søkt dig; la mig ikke fare vill fra dine bud!
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
I mitt hjerte har jeg gjemt ditt ord forat jeg ikke skal synde imot dig.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Lovet være du, Herre! Lær mig dine forskrifter!
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Med mine leber har jeg forkynt alle lover fra din munn.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Over dine vidnesbyrds vei har jeg gledet mig, som over all rikdom.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
På dine befalinger vil jeg grunde og tenke på dine stier.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
I dine forskrifter forlyster jeg mig, jeg glemmer ikke ditt ord.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Gjør vel imot din tjener, så jeg kan leve! Da vil jeg holde ditt ord.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Lat op mine øine, så jeg kan skue de underfulle ting i din lov!
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Jeg er en gjest på jorden; skjul ikke dine bud for mig!
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Min sjel er knust, så jeg lenges efter dine lover til enhver tid.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Du har truet de overmodige, de forbannede, som farer vill fra dine bud.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Ta skam og forakt bort fra mig! For jeg har tatt vare på dine vidnesbyrd.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Fyrster har også sittet og talt sammen imot mig; din tjener grunder på dine forskrifter.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Dine vidnesbyrd er også min lyst; de er mine rådgivere.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Min sjel er nedtrykt i støvet; hold mig i live efter ditt ord!
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Jeg fortalte dig mine veier, og du svarte mig; lær mig dine forskrifter!
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
La mig forstå dine befalingers vei! Så vil jeg grunde på dine undergjerninger.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Min sjel gråter av sorg; reis mig op efter ditt ord!
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Vend løgnens vei bort fra mig, og unn mig din lov!
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
Trofasthets vei har jeg utvalgt, dine lover har jeg satt for mig.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Jeg henger ved dine vidnesbyrd; Herre, la mig ikke bli til skamme!
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Dine buds vei vil jeg løpe; for du frir mitt hjerte fra angst.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Lær mig, Herre, dine forskrifters vei! Så vil jeg ta vare på den inntil enden.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Lær mig! Så vil jeg ta vare på din lov og holde den av hele mitt hjerte.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Led mig frem på dine buds sti! For i den har jeg min lyst.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Bøi mitt hjerte til dine vidnesbyrd og ikke til vinning!
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Vend mine øine bort fra å se efter tomhet, hold mig i live på din vei!
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Opfyll for din tjener ditt ord, som er for dem som frykter dig!
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Ta bort min vanære, som jeg frykter for! For dine lover er gode.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Se, jeg lenges efter dine befalinger; hold mig i live ved din rettferdighet!
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
La dine nådegjerninger, Herre, komme over mig, din frelse efter ditt ord!
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Jeg vil gi den svar som håner mig; for jeg setter min lit til ditt ord.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Ta ikke sannhets ord så rent bort fra min munn! For jeg bier på dine dommer.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Jeg vil holde din lov stadig, evindelig og alltid.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
La mig vandre i fritt rum! For jeg spør efter dine befalinger.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Jeg vil tale om dine vidnesbyrd for konger og skal ikke bli til skamme.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Jeg har min lyst i dine bud, som jeg elsker.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Jeg løfter mine hender til dine bud, som jeg elsker, og jeg vil grunde på dine forskrifter.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Kom i hu ordet til din tjener, fordi du har gitt mig håp!
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Det er min trøst i min elendighet at ditt ord har holdt mig i live.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
De overmodige har spottet mig såre; fra din lov er jeg ikke avveket.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Jeg kom dine dommer fra evighet i hu, Herre, og jeg blev trøstet.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
En brennende harme har grepet mig over de ugudelige, som forlater din lov.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Dine forskrifter er blitt mine lovsanger i min utlendighets hus.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Jeg kom om natten ditt navn i hu, Herre, og jeg holdt din lov.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Dette blev mig gitt: at jeg har tatt vare på dine befalinger.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Herren er min del, sa jeg, idet jeg holdt dine ord.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Jeg bønnfalt dig av hele mitt hjerte: Vær mig nådig efter ditt ord!
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
Jeg eftertenkte mine veier og vendte mine føtter til dine vidnesbyrd.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Jeg hastet og ventet ikke med å holde dine bud.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
De ugudeliges strikker har omspent mig, din lov har jeg ikke glemt.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Midt om natten står jeg op for å prise dig for din rettferdighets lover.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Jeg holder mig til alle dem som frykter dig, og som holder dine befalinger.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Jorden er full av din miskunnhet, Herre; lær mig dine forskrifter!
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Du har gjort vel imot din tjener, Herre, efter ditt ord.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Lær mig god skjønnsomhet og kunnskap! For jeg tror på dine bud.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Før jeg blev ydmyket, fór jeg vill; men nu holder jeg ditt ord.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Du er god og gjør godt; lær mig dine forskrifter!
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
De overmodige har spunnet løgn sammen imot mig; jeg holder dine befalinger av hele mitt hjerte.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Deres hjerte er som en fettklump; jeg har min lyst i din lov.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Det var mig godt at jeg blev ydmyket, forat jeg kunde lære dine forskrifter.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Din munns lov er mig bedre enn tusen stykker gull og sølv.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Dine hender har skapt mig og gjort mig; gi mig forstand, forat jeg må lære dine bud!
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
De som frykter dig, skal se mig og glede sig; for jeg venter på ditt ord.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Jeg vet, Herre, at dine dommer er rettferdighet, og i trofasthet har du ydmyket mig.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
La din miskunnhet være mig til trøst efter ditt ord til din tjener!
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
La din miskunnhet komme over mig, forat jeg kan leve! For din lov er min lyst.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
La de overmodige bli til skamme! For de har trykket mig ned uten årsak; jeg grunder på dine befalinger.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
La dem vende tilbake til mig, de som frykter dig og kjenner dine vidnesbyrd!
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
La mitt hjerte være fullkomment i dine forskrifter, forat jeg ikke skal bli til skamme!
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Min sjel vansmekter av lengsel efter din frelse; jeg venter på ditt ord.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mine øine vansmekter av lengsel efter ditt ord idet jeg sier: Når vil du trøste mig?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
For jeg er som en skinnsekk i røk; dine forskrifter glemmer jeg ikke.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Hvor mange er vel din tjeners dager? Når vil du holde dom over mine forfølgere?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
De overmodige har gravd graver for mig, de som ikke skikker sig efter din lov.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Alle dine bud er trofasthet; uten årsak forfølger de mig; hjelp mig!
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
På lite nær har de tilintetgjort mig i landet; men jeg har ikke forlatt dine befalinger.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Hold mig i live efter din miskunnhet! Så vil jeg ta vare på din munns vidnesbyrd.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Til evig tid, Herre, står ditt ord fast i himmelen.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Fra slekt til slekt varer din trofasthet; du grunnfestet jorden, og den stod der.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Til å utføre dine dommer står de der enn idag; for alle ting er dine tjenere.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Dersom din lov ikke hadde vært min lyst, var jeg omkommet i min elendighet.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Til evig tid skal jeg ikke glemme dine befalinger; for ved dem har du holdt mig i live.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Din er jeg, frels mig! For jeg har søkt dine befalinger.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
De ugudelige har bidd på mig for å ødelegge mig; jeg gir akt på dine vidnesbyrd.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
På all fullkommenhet har jeg sett en ende, men ditt bud strekker sig såre vidt.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Hvor jeg har din lov kjær! Hele dagen grunder jeg på den.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Dine bud gjør mig visere enn mine fiender; for til evig tid eier jeg dem.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Jeg er blitt klokere enn alle mine lærere; for jeg grunder på dine vidnesbyrd.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Jeg er forstandigere enn de gamle; for jeg har tatt vare på dine befalinger.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
Fra enhver ond sti har jeg holdt mine føtter borte forat jeg kunde holde ditt ord.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Fra dine lover er jeg ikke avveket; for du har lært mig.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Hvor dine ord er søte for min gane, mere enn honning for min munn!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Av dine befalinger får jeg forstand; derfor hater jeg all løgnens sti.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Ditt ord er en lykte for min fot og et lys for min sti.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
Jeg har svoret, og jeg har holdt det, å ta vare på din rettferdighets lover.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Jeg er såre nedbøiet; Herre, hold mig i live efter ditt ord!
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
La min munns frivillige offere tekkes dig, Herre, og lær mig dine lover!
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Jeg går alltid med livet i hendene, men din lov har jeg ikke glemt.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
De ugudelige har lagt snare for mig, men jeg har ikke forvillet mig fra dine befalinger.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Jeg har fått dine vidnesbyrd i eie evindelig; for de er mitt hjertes glede.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Jeg har bøiet mitt hjerte til å gjøre efter dine forskrifter evindelig, inntil enden.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
De tvesinnede hater jeg, men din lov elsker jeg.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Du er mitt skjul og mitt skjold, jeg venter på ditt ord.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Vik fra mig, I som gjør ondt, forat jeg må holde min Guds bud!
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Hold mig oppe efter ditt ord, forat jeg kan leve, og la mig ikke bli til skamme med mitt håp!
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Støtt mig, så jeg må bli frelst! Da vil jeg alltid skue med lyst på dine forskrifter.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Du akter for intet alle dem som farer vill fra dine forskrifter; for deres svik er forgjeves.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Som slagg bortrydder du alle ugudelige på jorden; derfor elsker jeg dine vidnesbyrd.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Av redsel for dig gyser min kropp, og jeg frykter for dine dommer.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
Jeg har gjort rett og rettferdighet; du vil ikke overgi mig til dem som undertrykker mig.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Gå i borgen for din tjener, forat det kan gå ham vel! La ikke de overmodige undertrykke mig!
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mine øine vansmekter av lengsel efter din frelse og efter din rettferdighets ord.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Gjør med din tjener efter din miskunnhet, og lær mig dine forskrifter!
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Jeg er din tjener; lær mig, så jeg kan kjenne dine vidnesbyrd!
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Det er tid for Herren å gripe inn; de har brutt din lov.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Derfor elsker jeg dine bud mere enn gull, ja mere enn fint gull.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Derfor holder jeg alle befalinger om alle ting for å være rette; jeg hater all løgnens sti.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Underfulle er dine vidnesbyrd; derfor tar min sjel vare på dem.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Dine ords åpenbaring oplyser, den gjør enfoldige forstandige.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Jeg åpnet min munn og sukket av lengsel; for jeg stundet efter dine bud.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Vend dig til mig og vær mig nådig, som rett er mot dem som elsker ditt navn!
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Gjør mine trin faste ved ditt ord, og la ingen urett herske over mig!
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Forløs mig fra menneskers vold! Så vil jeg holde dine befalinger.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
La ditt åsyn lyse for din tjener, og lær mig dine forskrifter!
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mine øine flyter bort i vannstrømmer over dem som ikke holder din lov.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Du er rettferdig, Herre, og dine dommer er rettvise.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Du har fastsatt dine vidnesbyrd i rettferdighet og stor trofasthet.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Min nidkjærhet har fortært mig, fordi mine motstandere har glemt dine ord.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ditt ord er vel renset, og din tjener elsker det.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Jeg er liten og foraktet; jeg har ikke glemt dine befalinger.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Din rettferdighet er en evig rettferdighet, og din lov er sannhet.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Nød og trengsel fant mig; dine bud er min lyst.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Dine vidnesbyrd er rettferdige til evig tid; lær mig, forat jeg kan leve!
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Jeg roper av hele mitt hjerte; svar mig, Herre! Jeg vil ta vare på dine forskrifter.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Jeg roper til dig, frels mig! Så vil jeg holde dine vidnesbyrd.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Jeg var årle oppe i morgenlysningen og ropte om hjelp; jeg ventet på dine ord.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mine øine var oppe før nattevaktene, forat jeg kunde grunde på ditt ord.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Hør min røst efter din miskunnhet! Herre, hold mig i live efter dine lover!
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
De er kommet nær som jager efter ugjerning; fra din lov er de kommet langt bort.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Du er nær, Herre, og alle dine bud er sannhet.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
For lenge siden vet jeg av dine vidnesbyrd at du har grunnet dem for evig tid.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Se min elendighet og utfri mig! For jeg har ikke glemt din lov.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Før min sak og forløs mig, hold mig i live efter ditt ord!
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Frelse er langt borte fra de ugudelige; for de søker ikke dine forskrifter.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Din miskunnhet er stor, Herre; hold mig i live efter dine dommer!
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Mange er mine forfølgere og mine motstandere; jeg er ikke avveket fra dine vidnesbyrd.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Jeg så de troløse og vemmedes, dem som ikke holdt ditt ord.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Se at jeg har elsket dine befalinger! Herre, hold mig i live efter din miskunnhet!
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Summen av ditt ord er sannhet, og til evig tid står all din rettferdighets lov fast.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Fyrster forfulgte mig uten årsak, men mitt hjerte fryktet for dine ord.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Jeg gleder mig over ditt ord som en som finner meget bytte.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Løgn har jeg hatet og avskydd, din lov har jeg elsket.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Syv ganger om dagen har jeg prist dig for din rettferdighets lover.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Megen fred har de som elsker din lov, og det er ikke noget anstøt for dem.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Jeg har ventet på din frelse, Herre, og jeg har holdt dine bud.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Min sjel har holdt dine vidnesbyrd, og jeg elsket dem såre.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
Jeg har holdt dine befalinger og dine vidnesbyrd; for alle mine veier er for ditt åsyn.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
La mitt klagerop komme nær for ditt åsyn, Herre! Lær mig efter ditt ord!
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
La min inderlige bønn komme for ditt åsyn! Frels mig efter ditt ord!
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mine leber skal flyte over av lovsang; for du lærer mig dine forskrifter.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Min tunge skal synge om ditt ord; for alle dine bud er rettferdighet.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
La din hånd være mig til hjelp! For jeg har utvalgt dine befalinger.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Jeg lenges efter din frelse, Herre, og din lov er min lyst.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
La min sjel leve og love dig, og la dine dommer hjelpe mig!
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Jeg har faret vill; opsøk din tjener som et tapt får! for jeg har ikke glemt dine bud.