< Zabura 119 >
1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Heureux ceux dont la conduite est intègre, Et qui suivent la loi de l'Éternel!
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Heureux ceux qui obéissent à ses enseignements, Qui le recherchent de tout leur coeur,
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Et qui ne commettent pas d'iniquité, Mais qui marchent dans les voies de l'Éternel!...
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Tu as donné tes commandements, ô Dieu, Pour qu'on les observe avec soin.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Daigne diriger ma conduite, Afin que j'observe tes préceptes!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Alors je n'aurai point à rougir, Quand je fixerai les regards sur tous tes commandements.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Je te célébrerai dans la droiture de mon coeur. Quand j'aurai appris tes justes jugements.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Je veux observer tes préceptes; Ne m'abandonne pas entièrement!
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Comment le jeune homme rendra-t-il pure sa conduite? C'est en restant fidèle à ta parole.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Je te cherche de tout mon coeur; Ne permets pas que je m'égare loin de tes commandements!
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
J'ai serré ta parole dans mon coeur. Afin de ne pas pécher contre toi.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Béni sois-tu, ô Éternel! Enseigne-moi tes préceptes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Mes lèvres énumèrent Tous les jugements que ta bouche a prononcés.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Je trouve autant de joie à suivre tes enseignements, Qu'à posséder tous les trésors du monde.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Je méditerai tes commandements, Et je fixerai mes regards sur tes sentiers.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Je ferai mes délices de tes préceptes, Et je n'oublierai point tes paroles.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Accorde ce bienfait à ton serviteur: que je vive. Et que je garde ta parole!
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Dessille mes yeux. Afin que je contemple les merveilles de ta loi.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Je suis étranger sur la terre; Ne me cache pas tes commandements!
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Mon âme est consumée par l'amour Que lui inspirent tes lois, en tout temps.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Tu menaces les orgueilleux, Ces maudits qui s'écartent de tes commandements.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Éloigne de moi l'opprobre et le mépris; Car j'obéis à tes enseignements.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Les puissants eux-mêmes se sont assis, Et ils ont parlé contre moi; Mais ton serviteur médite tes préceptes.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Oui, tes enseignements font mes délices: Ils sont mes meilleurs conseillers.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Mon âme est abattue dans la poussière; Fais-moi revivre, selon ta parole!
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Je t'ai fait connaître ma conduite, et tu m'as approuvé; Enseigne-moi tes préceptes.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Montre-moi la voie que tu m'ordonnes de suivre. Et je méditerai tes merveilles.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Mon âme attristée se fond en larmes; Relève-moi, selon ta parole!
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Éloigne-moi de la voie du mensonge; Accorde-moi comme une grâce la connaissance de ta loi!
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
J'ai choisi la voie de la fidélité; J'ai mis tes jugements devant mes yeux.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Je me suis attaché à tes enseignements: Éternel, ne me rends pas confus!
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Je m'élancerai dans la voie de tes commandements, Quand tu auras mis mon coeur au large.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Éternel, apprends-moi à suivre tes préceptes, Et je les observerai jusqu'à la fin.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Donne-moi l'intelligence, et j'observerai ta loi: Je la pratiquerai de tout mon coeur.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Conduis-moi dans les sentiers de tes commandements; Car mon bonheur est de les suivre.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline mon coeur vers tes enseignements. Et non pas vers le gain.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Détourne mes yeux de la contemplation des choses vaines; Que je trouve la vie en marchant dans tes voies.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Accomplis envers ton serviteur ta promesse: Tu l’as donnée pour qu’on te craigne.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Détourne de moi l'opprobre que je redoute; Car tes jugements sont pleins de bonté.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
J'ai un ardent amour pour tes commandements! Fais-moi revivre par ta justice!
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Éternel, que tes bontés et ton salut Descendent sur moi, selon ta promesse!
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Alors je saurai comment répondre à celui qui m'outrage; Car je me confie en ta parole.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Ne me refuse pas entièrement la faveur De rendre témoignage à la vérité; Car je mets mon attente en tes jugements.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Alors j'observerai ta loi constamment. Sans l'abandonner jamais.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Je marcherai d'un pas libre; Car j'ai à coeur de suivre tes commandements.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Je proclamerai tes volontés devant les rois. Et je n'en aurai aucune honte.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Je ferai mes délices de tes commandements: Ils sont l'objet de mon amour.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
J'élèverai mes mains vers tes commandements que j'aime. Et je méditerai tes préceptes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Souviens-toi de la parole donnée à ton serviteur C'est sur elle que tu as fondé mon espérance.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Ce qui me console dans mon affliction, C'est que ta parole me rend la vie.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Des orgueilleux me couvrent de railleries; Mais je ne m'écarte pas de ta loi.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Je me rappelle tes jugements d'autrefois, ô Éternel, Et j'y trouve ma consolation.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
L'indignation me saisit, à cause des méchants Qui abandonnent ta loi.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Tes préceptes sont le sujet de mes cantiques, Dans la maison où j'habite en étranger.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
La nuit, je me rappelle ton nom, ô Éternel, Et j'observe ta loi.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Le bien qui m'est échu en partage. C'est de garder tes commandements.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Tu es ma part, ô Éternel. C'est pourquoi j'ai promis de garder tes paroles.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Je t'ai imploré de tout mon coeur: Aie pitié de moi, selon ta promesse!
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
J'ai fait l'examen de ma conduite, Et j'ai dirigé mes pas dans la voie de tes enseignements.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Je me hâte, je ne diffère point D'observer tes commandements.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Les pièges des méchants m'ont environné; Je n'ai point oublié ta loi.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Au milieu de la nuit, je me lève pour te célébrer, A cause de tes justes jugements.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Je suis le compagnon de tous ceux qui te craignent Et qui observent tes commandements.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Éternel, la terre est pleine de ta bonté! Enseigne-moi tes préceptes.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Tu as fait du bien à ton serviteur, Éternel, selon ta parole.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Donne-moi un sens droit, ainsi que la vraie sagesse; Car j'ai foi en tes commandements.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Avant d'être affligé, je m'égarais; Mais, maintenant, j'observe ta parole.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Tu es bon, et tu manifestes ta bonté: Enseigne-moi tes préceptes.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Des orgueilleux ont ourdi contre moi des mensonges; Mais moi, j'obéis de tout mon coeur à tes ordres.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Leur coeur est épaissi comme de la graisse; Moi, je trouve mes délices dans ta loi.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Il m'est bon d'avoir été affligé: C'est ainsi que j'ai appris à connaître ta volonté.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Les enseignements de ta bouche sont plus précieux pour moi Que des milliers de pièces d'or et d'argent.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Toi dont les mains m'ont formé et créé, Donne-moi l'intelligence, afin que je puisse apprendre tes lois.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Ceux qui te craignent me verront, et ils se réjouiront; Car j'espère en ta parole.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Je sais, ô Éternel, que tes jugements ne sont que justice: C'est dans ta fidélité que tu m'as affligé.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Que ta bonté soit donc ma consolation. Comme tu l'as promis à ton serviteur.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Que tes compassions s'étendent sur moi, et je vivrai; Car ta loi fait mes délices.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Que les orgueilleux soient confus. Eux qui m'oppriment sans motif; Et moi, je méditerai tes commandements.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Qu'ils reviennent à moi, ceux qui te craignent Et qui connaissent tes enseignements!
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Que mon coeur soit sincèrement attaché à tes préceptes, Afin que je n'aie pas à rougir de honte!
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Mon âme languit après son salut; J'espère en ta parole.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mes yeux se consument dans l'attente de ta promesse; Je dis: «Quand me consoleras-tu?»
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Je suis comme une outre dans un nuage de fumée; Mais je n'oublie pas tes préceptes.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Combien courte est la vie de ton serviteur! Quand donc feras-tu justice de ceux qui me persécutent?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Les orgueilleux ont creusé des pièges sous mes pas; Car jamais ils n'agissent selon ta loi.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Tous tes commandements témoignent de ta fidélité. Mes ennemis me persécutent sans motif; aide-moi!
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Encore un peu, et ils me faisaient disparaître de la terre! Mais je n'abandonne pas tes commandements.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Fais-moi revivre, toi qui es plein de bonté. Et j'obéirai aux enseignements de ta bouche.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Éternel, ta parole subsiste à jamais dans les cieux;
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Ta fidélité dure d'âge en âge! Tu as fondé la terre, et elle demeure ferme.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Tout subsiste aujourd'hui selon tes lois; Car toutes choses te servent.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Si ta loi n'eût fait mes délices. J'aurais déjà péri dans ma misère.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Jamais je n'oublierai tes commandements; Car c'est par eux que tu m'as fait revivre.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Je suis à toi, sauve-moi; Car je m'applique à suivre tes commandements.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Les méchants m'ont épié pour me faire périr; Mais je suis attentif à tes enseignements.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
J'ai vu des bornes à tout ce qui est parfait; Mais ta loi est d'une étendue sans fin.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Combien j'aime ta loi! Tout le jour, je m'applique à la méditer.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Tes commandements me rendent plus sage Que mes ennemis, Parce qu'ils sont toujours présents à mon esprit.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
J'ai surpassé en sagesse tous ceux qui m'avaient instruit; Car tes enseignements sont l'objet de mes méditations.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Je suis plus intelligent que les vieillards eux-mêmes; Car j'ai gardé tes commandements.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
J'ai détourné mes pas de tout mauvais chemin, Afin d'observer ta parole.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Je ne m'écarte point de tes lois, Parce que c'est toi qui m'as instruit.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Combien tes paroles sont douces à mon palais, Plus douces que le miel à ma bouche!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Tes commandements m'instruisent; C'est pourquoi je hais tous les sentiers trompeurs.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Ta parole est un flambeau qui guide mes pas, Une lumière sur mon sentier.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
J'ai juré — et je tiendrai ma promesse. — D'observer tes justes lois.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Je suis extrêmement affligé: Éternel, fais-moi revivre, selon ta parole!
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Agrée les chants de louange Que t'offre ma bouche, ô Eternel, Et enseigne-moi tes commandements!
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Ma vie est continuellement en danger; Mais je n'oublie point ta loi.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Les méchants m'ont tendu des pièges; Mais je ne me suis pas écarté de tes commandements.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Tes enseignements sont pour toujours mon héritage; Ils sont la joie de mon coeur.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
J'ai rendu mon coeur docile à l'observation de tes préceptes, Pour toujours, jusqu'à la fin.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Je hais les hommes au coeur double; Mais j'aime ta loi.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Tu es mon refuge et mon bouclier; J'espère en ta parole.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Retirez-vous de moi, méchants! Je veux garder les commandements de mon Dieu.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Soutiens-moi, selon ta promesse, Afin que je vive, Et ne me fais pas rougir d'avoir mis en toi mon espérance!
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Soutiens-moi: je serai sauvé. Et j'aurai toujours les yeux sur tes préceptes!
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Tu traites avec mépris tous ceux qui s'écartent de tes lois; Car toutes leurs machinations sont frappées d'impuissance.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Tu rejettes, comme de l'écume. Tous les méchants de la terre. C'est pourquoi j'aime tes enseignements.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Ma chair tremble de frayeur en ta présence. Et je crains tes jugements.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
J'ai pratiqué ce qui est droit et juste; Ne m'abandonne pas à mes oppresseurs!
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Prends sous ta garde le bonheur de ton serviteur; Que les orgueilleux ne m'oppriment pas!
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mes yeux se consument dans l'attente de ton salut Et de tes promesses, ô Dieu juste.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Agis envers ton serviteur selon ta bonté, Et enseigne-moi tes préceptes.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Je suis ton serviteur; donne-moi l'intelligence, Afin que je puisse comprendre tes enseignements.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Le temps est venu d'agir en ta faveur, ô Éternel; Car on viole ta loi.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
C'est pourquoi j'aime tes commandements Plus que l'or, même que l'or fin.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Ainsi je proclame que tous tes commandements sont droits, Et je hais tout sentier trompeur.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Tes enseignements sont admirables; Aussi mon âme les met-elle en pratique.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Tes paroles sont une révélation qui éclaire; Elles donnent de l'intelligence aux simples.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
J'ouvre la bouche et je soupire; Car j'ai un grand amour pour tes commandements.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Regarde-moi et prends pitié de moi, Comme tu le fais pour ceux qui aiment ton nom.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Que ta parole affermisse mes pas. Et ne permets point que le péché domine sur moi.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Délivre-moi de l'oppression des hommes. Afin que j'observe tes commandements!
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Fais resplendir ta face sur ton serviteur, Et enseigne-moi tes préceptes!
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Des ruisseaux de larmes coulent de mes yeux. Parce que personne n'observe ta loi.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Tu es juste, ô Éternel, Et tes jugements sont droits.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Tu prescris avec force, dans tes enseignements, La justice et la fidélité.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Mon zèle me consume, Parce que mes ennemis ont oublié tes paroles.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ta parole est parfaitement pure; Aussi est-elle chère à ton serviteur.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Je suis petit et méprisé; Mais je n'oublie pas tes commandements.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Ta justice est une justice éternelle, Et ta loi n'est que vérité.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
La détresse et l'angoisse m'ont atteint; Mais tes commandements font mes délices.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Tes enseignements sont éternellement justes; Donne-m'en l'intelligence, afin que je vive!
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Je t'invoque de tout mon coeur; réponds-moi, ô Éternel, Et je garderai tes préceptes.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Je crie vers toi; sauve-moi, Et je suivrai tes enseignements.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Je devance l'aurore, et je t'invoque: Je mets mon espoir en ta parole.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mes yeux devancent les veilles de la nuit, Pour méditer ta promesse.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Dans ta bonté, ô Éternel, écoute ma voix; Dans ta justice, fais-moi revivre!
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Les voilà près de moi, ceux qui se précipitent dans le crime Et qui se détournent de ta loi.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Mais toi aussi, ô Éternel, tu t'approches de moi. Et tous tes commandements m'assurent de ta fidélité.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Depuis longtemps j'ai appris à connaître tes enseignements; Car tu les as établis pour toujours.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Regarde mon affliction, et délivre-moi; Car je n'ai pas oublié ta loi.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Défends ma cause, et délivre-moi; Fais-moi revivre, selon ta promesse!
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Le salut est loin des méchants. Parce qu'ils ne se soucient pas de tes préceptes.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Tes compassions sont en grand nombre, ô Éternel: Fais-moi revivre, suivant les arrêts de ta justice!
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Mes persécuteurs et mes adversaires sont nombreux; Mais je ne me détourne pas de tes enseignements.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
J'ai vu les infidèles, et j'en ai horreur: Ils n'observent pas ta parole.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Vois combien j'aime tes commandements; Éternel, fais-moi revivre, dans ta bonté!
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Ta parole tout entière n'est que vérité, Et tous les arrêts de ta justice sont éternels.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Les grands m'ont persécuté sans motif; Mais mon coeur n'a craint que tes paroles.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Je me réjouis de ta promesse. Comme celui qui a trouvé un grand trésor.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Je hais, j'ai en horreur le mensonge. Et j'aime ta loi.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Je te loue sept fois le jour. Pour les arrêts de ta justice.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Grande est la paix de ceux qui aiment ta loi: Rien ne peut les faire chanceler.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Éternel, j'attends ta délivrance, Et je pratique tes commandements.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Mon âme obéit à tes enseignements, Et je les aime d'un grand amour.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
J'observe tes commandements et tes lois; Car toute ma conduite est présente à tes yeux.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Éternel, que mon cri parvienne jusqu'à toi! Donne-moi l'intelligence, conformément à ta parole!
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Que ma supplication s'élève jusqu'à toi! Délivre-moi, suivant ta promesse!
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mes lèvres proclameront ta louange, Quand tu m'auras enseigné tes préceptes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Ma langue célébrera ta parole; Car tous tes commandements sont justes.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Étends ta main pour me venir en aide; Car je veux obéir à tes commandements.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Je soupire après ton salut, ô Éternel, Et ta loi fait mes délices.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Que mon âme vive, afin qu'elle te loue, Et que tes jugements soient mon appui!
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Je suis errant comme une brebis perdue: Viens à la recherche de ton serviteur! Car je n'ai pas oublié tes commandements!