< Zabura 119 >
1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Alléluiah! Heureux ceux qui, dans leur voie, conservent l'innocence, et cheminent en la loi du Seigneur.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Heureux ceux qui méditent ses témoignages, et qui le cherchent de toute leur âme.
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Car les ouvriers d'iniquité n'ont point marché dans ses voies.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Tu as intimé tes commandements, pour qu'ils soient scrupuleusement gardés.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Puissent mes voies être dirigées vers l'accomplissement de tes ordonnances!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Alors je ne serai point confondu, puisque j'aurai eu mes yeux sur tous tes commandements.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Je te rendrai gloire en la droiture de mon cœur, de ce que j'aurai appris les jugements de ta justice.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Je garderai tes ordonnances; ne me délaisse pas sans retour.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Comment le jeune homme maintiendra-t-il droite sa voie? En gardant tes paroles.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Je t'ai cherché de toute mon âme; ne me repousse pas de tes commandements.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
J'ai renfermé dans le secret de mon cœur toutes tes paroles pour ne point pécher contre toi.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Tu es béni, Seigneur, enseigne-moi tes préceptes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
J'ai publié de mes lèvres tous les jugements de ta bouche.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Je me suis complu dans la voie de tes témoignages, autant que dans la possession de toutes les richesses.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Je méditerai sur tes commandements, et je considèrerai tes voies.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
J'étudierai tes préceptes, et je n'oublierai point tes paroles.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Récompense ton serviteur; et je vivrai, et je garderai tes paroles.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Ote le voile de mes yeux, et je comprendrai les merveilles de ta loi.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Je suis passager sur la terre, ne me cache pas tes commandements.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Mon âme a brûlé, en tout temps, du désir de ta loi.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Tu as châtié les superbes; maudits soient ceux qui s'écartent de tes commandements.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Délivre-moi de l'opprobre et du mépris, car j'ai recherché tes témoignages.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Les princes se sont assis, et ils ont mal parlé de moi; mais ton serviteur méditait sur tes ordonnances.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Et tes témoignages sont mon étude, et tes conseils mon conseil.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Mon âme est attachée à la terre; vivifie-moi selon ta promesse.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Je t'ai fait connaître mes voies, et tu m'as écouté; enseigne-moi tes préceptes.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Apprends-moi la voie de tes préceptes, et je méditerai sur tes merveilles.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Mon âme s'est assoupie dans l'abattement; fortifie-moi de tes paroles.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Éloigne de moi la voie de l'iniquité, et fais-moi miséricorde à cause de ta loi.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
J'ai choisi la voie de la vérité, et je n'ai point oublié tes jugements.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Je me suis attaché à tes témoignages, Seigneur; ne m'humilie pas.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
J'ai couru dans la voie de tes commandements, lorsque tu as dilaté mon cœur.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Fais, Seigneur, que la voie de tes commandements soit ma loi, et je la chercherai toujours.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Donne-moi l'intelligence, et j'approfondirai ta loi, et je la garderai dans le fond de mon âme.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Guide-moi dans le sentier de tes commandements; car c'est celui-là que j'ai désiré.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline mon cœur vers tes témoignages, et non vers la convoitise.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Détourne mes yeux, pour qu'ils ne voient point les vanités; vivifie-moi en ta loi.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Confirme ta parole en ton serviteur, pour qu'il craigne de te déplaire.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Ôte-moi l'opprobre du péché que j'ai appréhendé; car tes jugements me sont délectables.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Voilà que j'ai désiré tes commandements; vivifie-moi en ta justice.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Seigneur, que ta miséricorde me vienne, et ton salut, comme tu me l'as promis.
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Et je pourrai répondre à ceux qui m'outragent, car j'ai espéré en tes paroles.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Ne retire point à jamais de ma bouche la parole de vérité, car j'ai surabondamment espéré en tes jugements.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Et je garderai ta loi toujours, dans tous les siècles des siècles.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Et je marchais au large, parce que j'avais recherché tes commandements.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Et devant les rois je parlais de tes témoignages, et je n'avais aucune honte.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Et je méditais tes commandements, que j'ai toujours tant aimés.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Et j'ai levé les mains vers tes commandements, que j'aime, et j'ai médité sur tes préceptes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Souviens-toi de tes paroles à ton serviteur; en elles tu m'as donné d'espérer.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Elles m'ont consolé dans mon abaissement, et ta parole m'a vivifié.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Les superbes ont agi envers moi avec une extrême injustice; mais je n'ai point dévié de ta loi.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Je me suis souvenu, Seigneur, de tes jugements éternels, et j'ai été consolé.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Le découragement m'a pris, à la vue des pécheurs qui abandonnaient ta loi.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Mais, dans le lieu de mon pèlerinage, je chantais encore tes préceptes.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Je me souvenais de ton nom, Seigneur, pendant la nuit, et je gardais ta loi.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Et cette grâce m'a été faite, parce que j'avais recherché tes préceptes.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Tu es mon partage, Seigneur; j'ai dit que je garderais ta loi.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
J'ai demandé de toute mon âme à voir ton visage; fais-moi miséricorde selon ta parole.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
J'ai pensé à tes voies, et j'ai tourné mes pas vers tes témoignages.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Je me suis préparé sans trouble à garder tes commandements.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Les liens des pécheurs m'ont enlacé; mais je n'ai point oublié ta loi.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Au milieu de la nuit, je me levais pour te rendre grâce de tes jugements et de tes ordonnances.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Je suis partisan de tous ceux qui te craignent et qui gardent tes commandements.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
La terre, Seigneur, est pleine de tes miséricordes; enseigne-moi tous tes préceptes.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Seigneur, tu as usé de bonté avec ton serviteur, selon ta parole.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Enseigne-moi la bonté, la discipline et la science, parce que j'ai eu foi en tes commandements.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Avant d'être humilié, j'ai failli; aussi ai-je gardé ta parole.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Tu es bon, Seigneur, et en ta bonté enseigne-moi tes ordonnances.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
L'iniquité des superbes s'est multipliée contre moi; pour moi, j'approfondirai tes commandements au fond de mon cœur.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Leur cœur s'est coagulé comme du laitage, et moi j'ai médité ta loi.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Il est heureux pour moi que tu m'aies humilié, pour que j'apprisse tes ordonnances.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
La loi qui sort de ta bouche est meilleure pour moi que des millions d'or et d'argent.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Ce sont tes mains qui m'ont formé et pétri; donne-moi l'intelligence, et je m'instruirai de tes commandements.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Ceux qui te craignent me verront, et ils seront réjouis, parce que j'ai surabondamment espéré en tes promesses.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Seigneur, je sais que tes jugements sont la justice même, et que tu m'as humilié selon ta vérité.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Et maintenant, que ta miséricorde me vienne et me console, comme tu l'as promis à ton serviteur.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Que tes miséricordes me viennent, et je vivrai, parce que ta loi est l'objet de ma méditation.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Qu'ils soient confondus, les superbes, parce qu'ils ont été injustes envers moi; pour moi, je méditerai sur tes commandements.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Que ceux qui te craignent viennent à moi, et ceux qui connaissent tes témoignages.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Qu'en tes préceptes mon cœur soit trouvé sans tache, pour que je ne sois point confondu.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Mon âme s'est épuisée à réclamer ton secours, tant j'avais espéré en tes paroles!
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mes yeux se sont éteints dans l'attente de ta parole, disant: Quand me consoleras-tu?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Me voici comme une outre pendant la gelée; et pourtant je n'ai point oublié tes préceptes.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Combien ton serviteur comptera-t-il encore de jours? Quand jugeras-tu ceux qui me persécutent?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Les méchants m'ont raconté des choses vaines; mais ce n'était point comme ta loi, Seigneur.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Tous tes commandements sont vérité; ils m'ont poursuivi injustement, protège-moi.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Peu s'en est fallu qu'ils ne m'aient achevé sur la terre; moi cependant je n'ai point délaissé tes commandements.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Vivifie-moi selon ta miséricorde, et je garderai les témoignages de ta bouche.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Seigneur, ta parole demeure dans le ciel éternellement;
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Ta vérité passe de génération en génération; tu as fondé la terre, et elle subsiste.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Comme tu l'as réglé, le jour continue de paraître; car tout t'obéit.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Si ta loi n'était point ma continuelle étude, je périrais dans l'humiliation.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Je n'oublierai jamais tes ordonnances, car en elles tu m'as vivifié.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Je suis à toi, sauve-moi; car j'ai recherché tes préceptes.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Les pécheurs m'ont épié pour me perdre; mais j'avais compris tes témoignages.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
J'ai vu la fin de toute œuvre, même la plus parfaite; seule ta loi est éternelle.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Que j'aime ta loi, Seigneur! elle est tout le jour l'objet de ma méditation.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Plus qu'à mes ennemis tu m'as fait goûter ta loi, car elle est toujours devant moi.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
J'ai eu plus d'intelligence que ceux qui m'ont instruit, car tes témoignages sont ma méditation.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
J'ai eu plus d'intelligence que les anciens, car j'ai cherché tes commandements.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
J'ai détourné mes pieds de toute voie mauvaise, afin de garder tes paroles.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Je n'ai point dévié de tes jugements, parce que tu as été mon législateur.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Que tes paroles sont douces à mon palais! elles le sont plus que le miel à ma bouche.
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Je tiens mon intelligence de tes préceptes; aussi ai-je en haine toute voie d'iniquité.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Ta loi est la lampe de mes pieds et la lumière de mes sentiers.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
J'ai juré et résolu de garder les jugements de ta justice.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
J'ai été profondément humilié, Seigneur; vivifie-moi selon ta parole.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Seigneur, aie pour agréables les offrandes volontaires de ma bouche, et enseigne-moi tes jugements.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Mon âme est toujours en tes mains, et je n'ai point oublié ta loi.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Les pécheurs m'ont tendu des pièges, et je n'ai point dévié de tes commandements.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
J'ai eu pour héritage éternel tes témoignages, et ils sont le tressaillement de mon cœur.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
J'ai incliné mon cœur à toujours agir selon tes ordonnances, en vue de ma rétribution.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Je hais les méchants, et j'aime ta loi.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Tu es mon champion et mon appui; j'ai surabondamment espéré en tes promesses.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Éloignez-vous de moi, pervers, et j'approfondirai les commandements de mon Dieu.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Soutiens-moi, Seigneur, selon ta parole, et vivifie-moi; et que je ne sois point confondu en mon attente.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Secours-moi, et je serai sauvé, et je méditerai toujours sur tes préceptes.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Tu as réduit à néant tous ceux qui se sont éloignés de tes jugements, parce que leur pensée est inique.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
J'ai compté comme pécheurs tous les prévaricateurs de la terre; c'est pourquoi j'aime tes témoignages.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Transperce mes chairs de ta crainte, car j'ai toujours redouté tes jugements.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
J'ai été droit dans mes jugements et ma justice; ne me livre pas à ceux qui me nuisent.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Affermis ton serviteur dans le bien; que les superbes ne le calomnient pas.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mes yeux ont défailli à force d'attendre mon salut et la parole de ton équité.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Traite ton serviteur selon ta miséricorde, et enseigne-moi tes préceptes.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Je suis ton serviteur; donne-moi l'intelligence, et je connaîtrai tes témoignages.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Le temps d'agir est venu pour le Seigneur; car ils ont renversé ta loi.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
C'est pour cela que j'ai aimé tes commandements plus que l'or et la topaze.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Aussi me suis-je dirigé selon tes commandements; j'ai pris en haine la voie de l'iniquité.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Tes témoignages sont merveilleux; aussi mon âme les a recherchés.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
La manifestation de tes paroles éclairera et instruira les plus jeunes enfants.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
J'ai ouvert la bouche, et je suis resté haletant du désir de tes commandements.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Regarde-moi, et faites-moi miséricorde, comme il est juste envers ceux qui aiment ton nom.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Dirige mes pas selon ta parole, et que nulle iniquité ne soit maîtresse de moi.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Délivre-moi des fausses accusations des hommes, et je garderai tes commandements.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Fais que brille ton visage sur ton serviteur, et enseigne-moi tes préceptes.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mes yeux se sont fondus en des torrents de larmes, parce que je n'avais point gardé ta loi.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Tu es juste, Seigneur, et tes jugements sont droits.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Tu nous as recommandé tes témoignages, comme étant la justice et la vérité.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Ton zèle m'a consumé, parce que mes ennemis avaient oublié tes paroles.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ta parole est éprouvée comme un feu ardent, et ton serviteur l'aime.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Et, quoique jeune et méprisé, je n'ai point oublié tes préceptes.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Ta justice est la justice éternelle, et ta loi, la vérité.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
La tribulation et la détresse sont venues me trouver; tes commandements ont été ma méditation.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Tes témoignages sont une justice éternelle; donne-m'en l'intelligence, et je vivrai.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
J'ai crié au fond de mon âme; exauce-moi, Seigneur, et je rechercherai tes préceptes.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
J'ai crié vers toi; sauve-moi, et je garderai tes témoignages.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Je me suis levé avant le jour, et j'ai crié, tant j'espérais en tes promesses.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mes yeux se sont ouverts avant l'aurore, pour méditer tes paroles.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Écoute ma voix. Seigneur, selon ta miséricorde; vivifie-moi selon ton jugement.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Mes persécuteurs se sont approchés de l'iniquité, et ils se sont éloignés de ta loi.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Tu es proche, Seigneur, et toutes tes voies sont vérité.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
J'ai reconnu dès le commencement, par tes témoignages, que tu les avais fondés pour tous les siècles.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Vois mon humiliation, et délivre-moi; car je n'ai point oublié ta loi.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Juge ma cause, et rachète-moi; vivifie-moi selon ta parole.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Le salut est loin des pécheurs, parce qu'ils n'ont point, recherché tes préceptes.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Tes miséricordes sont abondantes, Seigneur; vivifie-moi selon ton jugement.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Ceux qui me persécutent et m'oppriment sont nombreux; cependant je ne me suis point écarté de tes témoignages.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
J'ai vu les insensés, et je me suis consumé, parce qu'ils n'avaient point gardé tes paroles.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Vois, Seigneur, combien j'aime ta loi! vivifie-moi selon ta miséricorde.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
La vérité est le principe de tes paroles, et tous les jugements de ta justice sont éternels.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Les princes m'ont persécuté sans cause; mais mon cœur n'a redouté que tes paroles.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Je me réjouirai de tes paroles, comme celui qui trouve un riche butin.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Je hais l'iniquité, je l'ai en abomination; j'aime ta loi.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Sept fois le jour je t'ai loué, à cause des jugements de ta justice.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Ceux qui aiment ta loi jouissent d'une paix profonde, et il n'est point pour eux de scandale.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
J'ai attendu ton salut, Seigneur, et j'ai aimé tes commandements.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Mon âme a gardé tes témoignages; elle les a vivement aimés.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
J'ai gardé tes commandements et tes témoignages, parce que toutes mes voies sont en ta présence. Seigneur.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Que ma prière. Seigneur, arrive jusqu'à toi; donne-moi l'intelligence selon ta parole.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Que ma demande. Seigneur, arrive jusqu'à toi; délivre-moi selon ta parole.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Que mes lèvres chantent un hymne, quand tu m'auras enseigné tes préceptes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Que ma langue publie tes promesses, parce que tous tes commandements sont la justice.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Que ta main se prête à me sauver, parce que j'ai choisi ta loi.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
J'ai désiré ton salut. Seigneur, et ta loi est l'objet de ma méditation.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Mon âme vivra et te louera, et tes jugements seront mon soutien.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
J'ai été errant comme une brebis égarée; cherche ton serviteur, parce que je n'ai point oublié ta loi.